ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Mai Fada Da Cikawa

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

A karo na uku a dan tsakanin nan, wani babban jami’in Amurka na ziyara a kasar Sin. Sai dai a wannan karo, mai ziyarar shi ne jakadan Amurka mai kula da batun sauyin yanayi wato John Kerry. Ana sa ran yayin ziyararsa daga ranar 16 zuwa 19 ga wata, zai tattauna da bangaren kasar Sin kan batun sauyin yanayi, musamman game da yadda za a rage fitar da hayakin carbon a matsayinsu na kasashen da suka fi fitar da hayaki a duniya.

A ganina, ziyarar ta John Kerry ta zo a kan gaba, kuma a inda ya dace, la’akari da namijin kokarin da kasar Sin ke ci gaba da yi da zummar shawo kan matsalar.

  • Firaministan Sin Ya Gana Da Wakilin Amurka Kan Sauyin Yanayi

Wani abu da na fahimta dangane da kasar Sin shi ne, ba ta daukar alkawarin fatar baki, ita mai fada da cikawa ce. Ina sa ran kasar Sin za ta cimma burinta na kaiwa matsayin koli wajen fitar da hayakin carbon a shekarar 2030, tare da a samun daidaito tsakanin yawan hayakin da za ta fitar da abubuwan da za su shawo kansa ya zuwa 2060. Tabbas tuni kasar Sin ta dau hanya domin ta dade da fara aiwatar da abubuwa, kamar dashen bishiyoyi da dazuzukan da kyautata jituwa tsakanin dan adam da muhallinsa da sarrafa shawa da amfani da kyautata amfani da makamashi mai tsafta da sauransu. Ina da yakinin Sin za ta cimma burinta kafin lokacin da ta ayyana.

ADVERTISEMENT

Kuma na lura cikin dukkan wasu ayyukan kasar, ta kan mayar da hankali ne wajen ganin ta rage fitar da hayakin da ma duk wani abu da ka iya gurbata muhalli. Wannan ya tuna min da ziyarata ta baya-bayan nan a birnin Chengdu na lardin Sichuan, wato birnin da zai karbi bakuncin gasar wasannin daliban jami’o’i ta duniya, inda na ga yadda kasar ta shirya tsaf domin takaita abubuwan da ka iya gurbata muhalli. Misali, yadda motocin sufurin yayin gasar ke amfani da makamashi mai tsafta da yadda aka samar da na’urorin samar da lantarki daga makamashi mai tsafta da sauransu.

Haka zalika, su ma jama’ar kasar Sin suna kokarin rungumar hanyar da ta dace na rage fitar da hayaki mai guba. Misali, bayanai sun nuna cewa, a rabin farkon bana kadai, an yi wa kimanin sabbin motoci miliyan 3.13 masu amfani da sabon makamashi rejista, adadin da ya karu da kaso 41.6 a kan na bara, wanda kuma ya kai matsayin koli.

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Dama dai Amurka ce ke jan kafa kan batun sauyin yanayi inda take kokarin mayar da hannu agogo baya game da yarjejeniyoyin da aka cimma da kuma kin cika alkawurranta. Fatan ita ce yadda manyan jami’anta ke zarya a kasar Sin, ya kasance ta cika alkawuranta ta kuma dauki darasi daga kasar Sin, tare da hada hannu da ita wajen tabbatar da kafuwar duniya mai aminci da tsaro makoma ta bai daya ga daukacin bil adama.

 

 

Kasar Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Daga Birnin Sin

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Next Post
Gwamnan Zamfara Ya Kai Wa Mangal Ziyarar Ta’aziyya

Gwamnan Zamfara Ya Kai Wa Mangal Ziyarar Ta'aziyya

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.