• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Cafke Daliban Jami’a 3 Kan Kashe Direban Mota

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu daliban Jami’ar Bingham uku sun fada komar ‘yansanda kan zarginsu da kashe wani direban motar bolt da ya daukes u domin su sayo tabar wiwi a Abuja. 

Kisan nasa na zuwa ne bayan rashin jituwar da ta barke a tsakaninsu kan biyansu kudin jigilarsu da ya yi.

  • Halin ‘Yan Siyasa Na Ba Sarakuna Mamaki – Sarkin Zazzau
  • Gwamnatin Kaduna Ta Tabbatar Da Bullar Cutar Diphtheria A Kafanchan

Kwamishinan ‘yansandan birnin tarayya (FTC), Haruna Garba, shi ne ya tabbatar da hakan wa ‘yan jarida a ranar Alhamis.

A cewarsa, ‘yansanda sun samu rahoton gano gawar mamacin, Obasi Okeke, kwance macacce cikin jininsa a Ngugu Close, Area 11, Garki, Abuja.

A fadinsa, daya daga cikin wadanda ake zargin ne ya kira mamacin domin ya daukesu zuwa yankin Guzape da ke Abuja, sannan ya kaisu ya kuma dawo da su inda ya daukesu.

Labarai Masu Nasaba

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Ya ce, “A ranar 5 ga watan Yunin 2023, aka samu gangar jikin wani direba mai suna Obasi Okeke, kwance macacce cikin jininsa a Ngugu Close Area 11 Garki Abuja. ‘Yansanda sun dauki gawar domin kaddamar da bincike kan makasan direban.

“Binciken wadanda suka aikata wannan danyen aikin ya kai ga cafko wasu da ake zargi masu suna Obasieyene Inemesit Inem, Aaron Anthony da Alasan Ayomide Olusegun, wadanda dalibai ne na jami’ar Bingham, biyu daga cikin su ma su na matakin dakatarwa daga jami’ar.

“Daya daga cikin su ne ya kira direban domin ya kai su inda za su sayo tabar wiwi.

“Dawowarsu daga Guzape, inda ya daukesu. Sai suka fahimci ba su da kudin da za su biyu shi tukasu da ya yi, sai suka yanke shawarar yaudararsa ta hanyar nuna masa shaidar tura kudi na karya ‘debit alert’ a wayarsu, amma sai shi direban ya kage kai da fata cewa bai samu sakon kudi ba.

“A wannan gabar da suke takaddama, daya daga cikin wadanda ake zargin ya zaro wuka ya soka wa direban sai suka arce daga wajen.”

“Kuma tunin wadanda ake zargi su ukun suka amsa laifinsu, za mu gurfanar da su a gaban kuliya ba da jimawa ba,” a cewar CP.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbujaBoltDalibaiDirebaTabar Wiwi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Halin ‘Yan Siyasa Na Ba Sarakuna Mamaki – Sarkin Zazzau

Next Post

Xi Jinping Ya Ja Hankalin Kwararru A Fannonin Kimiyya Da Fasaha Da Su Mara Baya Da Yayata Ilimin Kimiyya

Related

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa
Manyan Labarai

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

21 seconds ago
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Labarai

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

2 hours ago
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

3 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

6 hours ago
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
Labarai

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

7 hours ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

17 hours ago
Next Post
Xi Jinping Ya Ja Hankalin Kwararru A Fannonin Kimiyya Da Fasaha Da Su Mara Baya Da Yayata Ilimin Kimiyya

Xi Jinping Ya Ja Hankalin Kwararru A Fannonin Kimiyya Da Fasaha Da Su Mara Baya Da Yayata Ilimin Kimiyya

LABARAI MASU NASABA

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.