ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Halin ‘Yan Siyasa Na Ba Sarakuna Mamaki – Sarkin Zazzau

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Siyasa

Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmed Nuhu Bamalli ya bayyana cewa halin ‘yan siyasa na bai wa sarakuna mamaki.

Mamakin da suke yi wa ‘yan siyasa, a cewarsa shi ne, lokacin da ‘yan siyasa ke yakin nema zabe sai su zo wurinsu, amma da zarar sun samu nasara ba a kara jin duriyarsu sai bayan shekaru hudu. Ya kara da cewa sarakuna na bukatar samun matsayi a tsarin mulki ba wai saboda yukurin kirkiro wani bangare na gwamnati ba ne a cikin kasar nan.

  • Gwamnatin Kaduna Ta Tabbatar Da Bullar Cutar Diphtheria A Kafanchan

Sarkin Zazzau ya bayyana hakan ne a lokacin da shugaban majalisar wakilai, Rt. Hon Tajudeen Abbas ya ziyarce shi a fadarsa da ke Zariya ta Jihar Kaduna.

ADVERTISEMENT

“Ba za a iya bata kwatanta irin gudummuwar da sarakuna suke bayarwa ba, saboda sarakuna suna taka muhimmiyar rawa tun fara mulkin dimokuradiyya har zuwa yau. Na san cewa mafi yawancinku a nan kuna da alaka da sakakuna ko ta kusa ko ta nesa.

“Abin da yake ba mu mamaki shi ne, mutane suna zuwa wurinmu neman tabarraki lokacin zabe, amma da zarar sun samu nasara, ba za su sake dawowa ba sai lokacin zabe kana su kara tuntubarmu. Kafin yanzu, muna mamakin yadda ake yi wa sarakuna haka, amma kuma sun kasa ganewa cewa su sarakuna a ko da yaushe suna nan kan mukaminsu, ko muna raye ko mun mutu. Duk inda mutum ya je sai ya dawo wurinmu.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

“Muna jin yadda wasu ‘yan siyasa ke cewa muna son kirkiro wani bangare na gwamnati. Ina magana amadadin sauran sarakuna kamar irinsu Mai Alfarma Sarkin Musulmi da Shehun Borno da sauran sarakuna. Mun tattauna kan wannan matsala babu adadi.

Mun je Abuja, inda muka gana da tsohon shugaban kasa da shugaban majalisar dattawa da shugaban majalisar wakilai. Mun gabatar da matsayinmu karkashin jagorancin Sarkin Lafiya wanda shi tsohon alkalin kotun koli ne. Mun zayyana matsayinmu, inda muka mika wa tsohon shugaban majalisar dattawa, mun yi mamakin yadda aka yi watsi da kudurin namu.

“Ina magana ne amadadin daukacin sarakunan Arewa. Muna fatan majalisar kasa da duba wannan kurin tare da aiki a kansa da kuma tabbatar ya zama doka.”
Ya kara da cewa babu abin da Masarautar Zazzau za ta iya cewa sai dai godiya ga Allah da ya azurtata.

Ya ce masarautar da kyankyashe shahararrun ‘yan Nijeriya tun daga kan tsohon shugaban kasa, Yakubu Gowon da tsohon mataimakin shugaban kasa, Namadi Sambo da ministoci da dama da sakatarorin gwamnatin tarayya, yanzu kuma ga shugaban majalisar wakilai.

Da yake jawabi, Rt. Hon Tajudeen Abbas ya sha alwashin cewa majalisa ta 10 za ta karkiri matsayin sarakuna a cikin kundin tsarin mulkin kasar nan.

Shugaban majalisar wakilai wanda shi dan asalin garin Zariya ne da yake wakiltar mazabar Zariya a zauren majalisa kuma yana da sarauta a cikin masarautar. Ya ce shi da kansa da kuma sauran ‘yan majalisan wakilai sun fahimci muhimmancin sarakuma, sannan za su tabbatar da cewa sun saka su a cikin kundin tsarin mulki.

“Tun shekaru uku da suka gabata na san cewa akwai takardar da majalisar sarakunan kasar nan suka gabatar, inda suka bayyana yadda sarakuna ya kamata su yi aiki a wannan zamani. Muna yi wa Allah godiya da ya kaddara danku ya zama shugaban majalisar wakilai kuma zai sake yin nazari kan matsayin sarakuna.

“Ina mai tabbatar muka cewa ni da suran ‘yan majalisa za mu sake bankado takardar da majalisar sarakuna ta rubuta domin tabbatar da cewa an sama aikin sarakuna a cikin kundin tsarinmulki.

“Za mu yi aiki kafada da kafada da dukkan majalisun kasa domin sake dawo da martabar sarakunan gargajiya.”
Ya nuna jin dadinsa ga sarkin da kuma daukacin mutanen masarautar Zazzau bisa wannan ziyara ta farko tun bayan da ya zama shugaban majalisar wakilai.

Siyasa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

'Yansanda Sun Cafke Daliban Jami'a 3 Kan Kashe Direban Mota

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.