ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Halin ‘Yan Siyasa Na Ba Sarakuna Mamaki – Sarkin Zazzau

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Siyasa

Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmed Nuhu Bamalli ya bayyana cewa halin ‘yan siyasa na bai wa sarakuna mamaki.

Mamakin da suke yi wa ‘yan siyasa, a cewarsa shi ne, lokacin da ‘yan siyasa ke yakin nema zabe sai su zo wurinsu, amma da zarar sun samu nasara ba a kara jin duriyarsu sai bayan shekaru hudu. Ya kara da cewa sarakuna na bukatar samun matsayi a tsarin mulki ba wai saboda yukurin kirkiro wani bangare na gwamnati ba ne a cikin kasar nan.

  • Gwamnatin Kaduna Ta Tabbatar Da Bullar Cutar Diphtheria A Kafanchan

Sarkin Zazzau ya bayyana hakan ne a lokacin da shugaban majalisar wakilai, Rt. Hon Tajudeen Abbas ya ziyarce shi a fadarsa da ke Zariya ta Jihar Kaduna.

ADVERTISEMENT

“Ba za a iya bata kwatanta irin gudummuwar da sarakuna suke bayarwa ba, saboda sarakuna suna taka muhimmiyar rawa tun fara mulkin dimokuradiyya har zuwa yau. Na san cewa mafi yawancinku a nan kuna da alaka da sakakuna ko ta kusa ko ta nesa.

“Abin da yake ba mu mamaki shi ne, mutane suna zuwa wurinmu neman tabarraki lokacin zabe, amma da zarar sun samu nasara, ba za su sake dawowa ba sai lokacin zabe kana su kara tuntubarmu. Kafin yanzu, muna mamakin yadda ake yi wa sarakuna haka, amma kuma sun kasa ganewa cewa su sarakuna a ko da yaushe suna nan kan mukaminsu, ko muna raye ko mun mutu. Duk inda mutum ya je sai ya dawo wurinmu.

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

“Muna jin yadda wasu ‘yan siyasa ke cewa muna son kirkiro wani bangare na gwamnati. Ina magana amadadin sauran sarakuna kamar irinsu Mai Alfarma Sarkin Musulmi da Shehun Borno da sauran sarakuna. Mun tattauna kan wannan matsala babu adadi.

Mun je Abuja, inda muka gana da tsohon shugaban kasa da shugaban majalisar dattawa da shugaban majalisar wakilai. Mun gabatar da matsayinmu karkashin jagorancin Sarkin Lafiya wanda shi tsohon alkalin kotun koli ne. Mun zayyana matsayinmu, inda muka mika wa tsohon shugaban majalisar dattawa, mun yi mamakin yadda aka yi watsi da kudurin namu.

“Ina magana ne amadadin daukacin sarakunan Arewa. Muna fatan majalisar kasa da duba wannan kurin tare da aiki a kansa da kuma tabbatar ya zama doka.”
Ya kara da cewa babu abin da Masarautar Zazzau za ta iya cewa sai dai godiya ga Allah da ya azurtata.

Ya ce masarautar da kyankyashe shahararrun ‘yan Nijeriya tun daga kan tsohon shugaban kasa, Yakubu Gowon da tsohon mataimakin shugaban kasa, Namadi Sambo da ministoci da dama da sakatarorin gwamnatin tarayya, yanzu kuma ga shugaban majalisar wakilai.

Da yake jawabi, Rt. Hon Tajudeen Abbas ya sha alwashin cewa majalisa ta 10 za ta karkiri matsayin sarakuna a cikin kundin tsarin mulkin kasar nan.

Shugaban majalisar wakilai wanda shi dan asalin garin Zariya ne da yake wakiltar mazabar Zariya a zauren majalisa kuma yana da sarauta a cikin masarautar. Ya ce shi da kansa da kuma sauran ‘yan majalisan wakilai sun fahimci muhimmancin sarakuma, sannan za su tabbatar da cewa sun saka su a cikin kundin tsarin mulki.

“Tun shekaru uku da suka gabata na san cewa akwai takardar da majalisar sarakunan kasar nan suka gabatar, inda suka bayyana yadda sarakuna ya kamata su yi aiki a wannan zamani. Muna yi wa Allah godiya da ya kaddara danku ya zama shugaban majalisar wakilai kuma zai sake yin nazari kan matsayin sarakuna.

“Ina mai tabbatar muka cewa ni da suran ‘yan majalisa za mu sake bankado takardar da majalisar sarakuna ta rubuta domin tabbatar da cewa an sama aikin sarakuna a cikin kundin tsarinmulki.

“Za mu yi aiki kafada da kafada da dukkan majalisun kasa domin sake dawo da martabar sarakunan gargajiya.”
Ya nuna jin dadinsa ga sarkin da kuma daukacin mutanen masarautar Zazzau bisa wannan ziyara ta farko tun bayan da ya zama shugaban majalisar wakilai.

Siyasa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

'Yansanda Sun Cafke Daliban Jami'a 3 Kan Kashe Direban Mota

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.