• English
  • Business News
Friday, August 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Na Bukatar Hazakar Kissinger A Harkokin Diplomasiyya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Amurka Na Bukatar Hazakar Kissinger A Harkokin Diplomasiyya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jiya Alhamis shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da tsohon sakataren harkokin wajen kasar Amurka Henry Kissinger a birnin Beijing, hedkwatar kasar, inda ya kira Kissinger mai shekaru 100 da haihuwa tsohon aboki, tare da yaba wa gagarumar gudummowarsa a fannonin kara azama kan ci gaban hulda a tsakanin Sin da Amurka, da kyautata zumuncin da ke tsakanin al’ummomin kasashen 2. 

Yau shekaru 52 da suka wuce, Kissinger ya kasance mai ba da taimako ga shugaba Richard Nixon na Amurka na wancan lokaci ta fuskar tsaron kasa, da kuma manzon musamman, ya gana da tsoffin shugabannin kasar Sin, matakin da ya kaddamar da aikin maido da hulda tsakanin Sin da Amurka yadda ya kamata.

  • Xi Jinping Ya Ja Hankalin Kwararru A Fannonin Kimiyya Da Fasaha Da Su Mara Baya Da Yayata Ilimin Kimiyya

Ya zuwa yanzu, Kissinger ya ziyarci kasar Sin fiye da sau 100. Tsohon mai shekaru 100 da haihuwa, yana himmantuwa wajen kyautata tuntubar juna tsakanin Sin da Amurka.

Cikin ‘yan siyasar Amurka, Kissinger ya wakilci rukunin wadanda suke nacewa kan tattaunawa da kasar Sin, da kuma daidaita sabani yadda ya kamata. Wadannan ‘yan siyasan sun tsara manufofi masu dacewa game da kasar Sin bisa sanin ya kamata, a kokarin kiyaye muradun Amurka.

A duk lokacin da yake zantawa da shugaba Joe Biden na Amurka ta wayar tarho, ko kuma fuska da fuska, ko lokacin ganawarsa da mista Kissinger a jiya, shugaba Xi Jinping ya sha nanata cewa, dole ne a bi ka’idoji 3 wajen raya hulda a tsakanin Sin da Amurka ba tare da wata matsala ba, wato mutunta juna, da zaman tare cikin lumana, da yin hadin gwiwa domin samun nasara tare. Su ne kuma darussan da aka koya daga yadda Sin da Amurka suka yi mu’amala da juna a baya, kana kuma, ka’idoji ne da kasashen 2 za su bi a sabon zamani, yayin da suke mu’amala da juna.

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

Yanzu haka kusoshin Amurka suna bukatar yin bitar abubuwan da suka faru a tarihi, kuma su kara sanin yadda suke kallon kasar Sin yadda ya kamata, da yadda za su yi mu’amala da kasar Sin, a kokarin biyan bukatunta. Idan sun san amsar hakan, fannonin hadin gwiwa a tsakanin Amurka da Sin za su fadada, ba wai ta fuskar daidaita rikici kadai ba. Ko shakka babu, Amurka na bukatar hazakar Kissinger wajen raya hulda a tsakanin Sin da Amurka. (Tasallah Yuan)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Marseille Ta Dauki Aubameyang Daga Chelsea

Next Post

Sin Ta Dawo Da Wadanda Suka Aikata Cin Hanci 582 Da Suka Gudu Zuwa Ketare

Related

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

8 minutes ago
Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?
Daga Birnin Sin

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

1 hour ago
Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe
Daga Birnin Sin

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

2 hours ago
An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

3 hours ago
Sin Ta Gabatar Da Korafi Da Babbar Murya Dangane Da Kalaman Jagoran Philippines 
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Korafi Da Babbar Murya Dangane Da Kalaman Jagoran Philippines 

4 hours ago
Xi Ya Bukaci A Yi Dukkan Mai Yiwuwa Wajen Gudanar Da Ayyukan Bincike Da Ceto Bayan Aukuwar Ambaliya A Lardin Gansu
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci A Yi Dukkan Mai Yiwuwa Wajen Gudanar Da Ayyukan Bincike Da Ceto Bayan Aukuwar Ambaliya A Lardin Gansu

5 hours ago
Next Post
Sin Ta Dawo Da Wadanda Suka Aikata Cin Hanci 582 Da Suka Gudu Zuwa Ketare

Sin Ta Dawo Da Wadanda Suka Aikata Cin Hanci 582 Da Suka Gudu Zuwa Ketare

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

August 8, 2025
Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

August 8, 2025
Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

August 8, 2025
Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

August 8, 2025
Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

August 8, 2025
Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

August 8, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

August 8, 2025
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

An Hallaka Manomi, An Kashe Shanu Da Tumakai A Wani Sabon Rikici A Bogoro

August 8, 2025
An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

August 8, 2025
Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.