• English
  • Business News
Tuesday, August 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mene Ne Ainihin Makasudin Ziyarar Manyan Jami’an Amurka A Yankin Kudancin Tekun Pasifik?

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Mene Ne Ainihin Makasudin Ziyarar Manyan Jami’an Amurka A Yankin Kudancin Tekun Pasifik?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jiya Laraba 26 ga wata, sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken, ya halarci bikin kaddamar da sabon ofishin jakadancin Amurka dake kasar Tonga, al’amarin da ya zama karo na farko da aka bude irin wannan ofishin jakadanci, tun bayan da kasashen biyu suka kulla huldar diflomasiyya shekaru 51 da suka gabata. A dai jiyan, ministan tsaron Amurka Lloyd Austin, ya ziyarci kasar Papua New Guinea, kana jami’an Amurkar biyu za su hadu a kasar Australiya, don halartar shawarwarin shekara-shekara da ake kira “2+2” tare da bangaren Australiya. A ‘yan shekarun nan, Amurka na kara mayar da hankali ga halartar harkokin yankin kudancin tekun Pasifik.

Ba’a dai taba ganin irin wannan kwazo na Amurka a wannan yanki cikin shekaru da dama da suka gabata ba. Amma abun tambaya shi ne, yaushe ne Amurka ta sauya manufar ta game da wannan yanki?

A zahiri take cewa a ‘yan shekarun nan, kasar Sin na kara hada kai tare da kasashe tsibiran tekun Pasifik bisa tushen girmama juna, al’amarin da ya samu maraba sosai daga gwamnatoci gami da al’ummun kasashen, yayin da ita Amurka ke nuna damuwa sosai, har ma ta sauke girman kai, da rashin kulawar da take nuna ga yankin, kana ta fara tura wasu manyan jami’anta don ziyartar wadannan kasashe, da yi musu alkawarin samun babban tallafi.

Amma mene ne ainihin makasudin Amurka na yin hakan? Jaridar Washington Post ta nuna cewa, makasudin shi ne shawo kan muhimmiyar rawar da kasar Sin ke kara takawa a wannan yanki. Kana, akwai manazarta da suka bayyana cewa, Amurka na son lalata moriyar kasar Sin a yankin kudancin tekun Pasifik, tare da kawo tsaiko ga hadin-gwiwarta da kasashen yankin.

Amurka ta kirkiro abun da take kira “barazana daga kasar Sin”, da zummar tilastawa kasashen yankin kudancin tekun Pasifik gudanar da harkokinsu bisa ra’ayinta, amma ta raina kudirin kasashen na tsayawa neman ci gaba cikin ‘yanci. Kamar dai yadda firaministan tsibirin Solomon, Manasseh Sogavare ya ce, “babu wani abun da zai iya hana hadin-gwiwar sada zumunta tsakanin kasarsa da kasar Sin.” (Murtala Zhang)

Labarai Masu Nasaba

An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK

Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kutsen Yanar Gizo Da Take Kaiwa Sin Ya Shaida Damuwar Amurka A Fannin Tsaro

Next Post

Manyan Ayyukan Tasoshin Teku Da Aka Watsar A Nijeriya…

Related

An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK
Daga Birnin Sin

An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK

18 hours ago
Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli
Daga Birnin Sin

Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

19 hours ago
Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 
Daga Birnin Sin

Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 

20 hours ago
Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista

21 hours ago
Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro
Daga Birnin Sin

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

23 hours ago
Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK
Daga Birnin Sin

Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK

2 days ago
Next Post
Manyan Ayyukan Tasoshin Teku Da Aka Watsar A Nijeriya…

Manyan Ayyukan Tasoshin Teku Da Aka Watsar A Nijeriya…

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Miliyan 14 Sun Yi Bikin Murnar Karɓar Kyautar N23m Daga Bankin STANBIC IBTC

‘Yan Nijeriya Miliyan 14 Sun Yi Bikin Murnar Karɓar Kyautar N23m Daga Bankin STANBIC IBTC

August 12, 2025
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

August 12, 2025
An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami

An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami

August 12, 2025
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

Jagora A ADC Ya Ƙaryata Zargin Atiku Ya Kankane Komai A Jam’iyyar

August 12, 2025
’Yan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 6 A Taraba

’Yan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 6 A Taraba

August 12, 2025
Sadiq Umar Da Bello El-Rufai Sun Sayi Ƙungiyar Rancher Bees FC Ta Kaduna

Sadiq Umar Da Bello El-Rufai Sun Sayi Ƙungiyar Rancher Bees FC Ta Kaduna

August 12, 2025
Ba Iya Yunwa Ce Kaɗai Ke Kashe Ƙananan Yara A Katsina Ba – Gwamnati

Ba Iya Yunwa Ce Kaɗai Ke Kashe Ƙananan Yara A Katsina Ba – Gwamnati

August 12, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Batun Rashin Lafiyar Tinubu

August 12, 2025
Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

August 11, 2025
Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

August 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.