• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Reshen Jihar Ribas Ta Kaddamar Da “Operation Tsaron Iyaka”

by yahuzajere
2 years ago
NIS

Kwanturolan Hukumar Kula da Shige da Fice ta Jihar Ribas (NIS) James Sunday, ya yi wa manema labarai karin haske kan fara aikin “Operation Tsaron Iyaka” a Jihar Ribas.

Kwanturolan ya ce hakan ya samo asali ne daga ganawar da suka yi a jihar Akwa Ibom da mukaddashiyar kwanturola Janar ta Hukumar Shige da Fice, Caroline Wuraola Adepoju wadda ta kai ziyarar aiki ta kwanaki 2 a Akwa Ibom kuma ta ziyarci ofishin kula da iyakoki na ruwa a jihar.
Sauran manyan jami’ai masu mukamin Kwanturola na Shiyyar E na Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya na cikin tawagarta, musamman Kwanturola Akwa Ibom, Abia, Cross River, Ebonyi, Rivers da na Sashen Kula da Iyaka ta Ruwa da ke Jihar Akwa Ibom.

  • “Da Mijina Ya Yi Min Kishiya, Gwamma Ya Rika Kwanciya Da ‘Ya`yanmu”

An yi ziyarar ce domin tantance ayyukan bakin iyaka, ayyuka da ayyukan tattalin arziki da aka gudanar a jihar Rivers kasancewar jihar a gabar ruwa.

Kwanturola James Sunday, ya ce “Operation Tsaron Iyaka” wanda ke nuni da karfafa tsaron kan iyaka shi ne abin da zai fi mayar da hankali a kai sakamakon taron da suka yi da kuma amfani da umarnin da mukaddashiyar Kwanturola Janar ta Hukumar Kula da Shige da Fice Caroline Wuraola Adepoju ta bayar, shi ya sa na yanke shawarar fara aikin tare da jami’anmu a Jihar Ribas.

“Jami’amu za su kai samame a wurare da maboya da tashar jiragen ruwa inda ake zargin ‘yan kasar waje da suka shigo Nijeriya ba bisa ka’ida ba suna boye a nan, tare da cafke su da gurfanar da duk wani mutum ko rukuni na bakin haure da aka gano suna zaune ba tare da ingantattun takardu na shigowa ba.

LABARAI MASU NASABA

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

“Za mu bazama aiki a wannan yunkuri na kawar da ‘yan ci-rani ba bisa ka’ida ba a Jihar Ribas wadanda za su iya shiga aikata cikin munanan ayyuka tare da gujewa gano su a duk lokacin da suka aikata wani laifi ko kuma suka shiga cikin wani abu mara kyau wanda na iya kaiwa ga rashin tsaro ga rayuwa da dukiyoyin mutane a Ribas.” In ji shi.

Sanarwar manema labarai da jami’in hulda da jama’a na reshen hukumar ta NIS da ke JIhar Ribas, ASI Nwosu Chukwu ya fitar, ta kara da cewa hukumar ta fara aiki nan take, kuma za ta ci gaba da aiki har sai ta gamsu da cewa ‘yan ci-rani ba bisa ka’ida ba sun tafi da kansu wuraren da suka kamata domin tsara takardunsu da kuma al’ummarsu ta bin ka’idar ECOWAS da sauran su, da aka shimfida bisa tanade-tanade na Dokar Shige da Fice ta 2015 da Dokokin 2017 da sauran manyan dokokin kasar.

Kwanturola James ya ba da tabbacin masu bin doka da oda daa cikin ‘yan ci-ranin a kullum suna ba su kariya da harkokin kasuwancinsu da rayuwarsu da dukiyoyinsu a Ribas sannan ya shawarci al’umma ko shugabannin kungiyoyi da su fito da jerin sunayen mambobinsu na jihar Ribas domin tabbatar da cewa kowa ya yi rajistar da ta kamata a hukumar ta Shige da Fice (NIS).

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri
Labarai

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar
Manyan Labarai

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
Labarai

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

October 24, 2025
Next Post
Tsadar Mai: Ba Gudu Ba Ja Da Baya Kan Zanga-Zanga -NLC

Tsadar Mai: Ba Gudu Ba Ja Da Baya Kan Zanga-Zanga -NLC

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

October 24, 2025
Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

October 24, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

October 24, 2025
Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

October 24, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.