ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Reshen Jihar Ribas Ta Kaddamar Da “Operation Tsaron Iyaka”

by yahuzajere
3 years ago
NIS

Kwanturolan Hukumar Kula da Shige da Fice ta Jihar Ribas (NIS) James Sunday, ya yi wa manema labarai karin haske kan fara aikin “Operation Tsaron Iyaka” a Jihar Ribas.

Kwanturolan ya ce hakan ya samo asali ne daga ganawar da suka yi a jihar Akwa Ibom da mukaddashiyar kwanturola Janar ta Hukumar Shige da Fice, Caroline Wuraola Adepoju wadda ta kai ziyarar aiki ta kwanaki 2 a Akwa Ibom kuma ta ziyarci ofishin kula da iyakoki na ruwa a jihar.
Sauran manyan jami’ai masu mukamin Kwanturola na Shiyyar E na Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya na cikin tawagarta, musamman Kwanturola Akwa Ibom, Abia, Cross River, Ebonyi, Rivers da na Sashen Kula da Iyaka ta Ruwa da ke Jihar Akwa Ibom.

  • “Da Mijina Ya Yi Min Kishiya, Gwamma Ya Rika Kwanciya Da ‘Ya`yanmu”

An yi ziyarar ce domin tantance ayyukan bakin iyaka, ayyuka da ayyukan tattalin arziki da aka gudanar a jihar Rivers kasancewar jihar a gabar ruwa.

ADVERTISEMENT

Kwanturola James Sunday, ya ce “Operation Tsaron Iyaka” wanda ke nuni da karfafa tsaron kan iyaka shi ne abin da zai fi mayar da hankali a kai sakamakon taron da suka yi da kuma amfani da umarnin da mukaddashiyar Kwanturola Janar ta Hukumar Kula da Shige da Fice Caroline Wuraola Adepoju ta bayar, shi ya sa na yanke shawarar fara aikin tare da jami’anmu a Jihar Ribas.

“Jami’amu za su kai samame a wurare da maboya da tashar jiragen ruwa inda ake zargin ‘yan kasar waje da suka shigo Nijeriya ba bisa ka’ida ba suna boye a nan, tare da cafke su da gurfanar da duk wani mutum ko rukuni na bakin haure da aka gano suna zaune ba tare da ingantattun takardu na shigowa ba.

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

“Za mu bazama aiki a wannan yunkuri na kawar da ‘yan ci-rani ba bisa ka’ida ba a Jihar Ribas wadanda za su iya shiga aikata cikin munanan ayyuka tare da gujewa gano su a duk lokacin da suka aikata wani laifi ko kuma suka shiga cikin wani abu mara kyau wanda na iya kaiwa ga rashin tsaro ga rayuwa da dukiyoyin mutane a Ribas.” In ji shi.

Sanarwar manema labarai da jami’in hulda da jama’a na reshen hukumar ta NIS da ke JIhar Ribas, ASI Nwosu Chukwu ya fitar, ta kara da cewa hukumar ta fara aiki nan take, kuma za ta ci gaba da aiki har sai ta gamsu da cewa ‘yan ci-rani ba bisa ka’ida ba sun tafi da kansu wuraren da suka kamata domin tsara takardunsu da kuma al’ummarsu ta bin ka’idar ECOWAS da sauran su, da aka shimfida bisa tanade-tanade na Dokar Shige da Fice ta 2015 da Dokokin 2017 da sauran manyan dokokin kasar.

Kwanturola James ya ba da tabbacin masu bin doka da oda daa cikin ‘yan ci-ranin a kullum suna ba su kariya da harkokin kasuwancinsu da rayuwarsu da dukiyoyinsu a Ribas sannan ya shawarci al’umma ko shugabannin kungiyoyi da su fito da jerin sunayen mambobinsu na jihar Ribas domin tabbatar da cewa kowa ya yi rajistar da ta kamata a hukumar ta Shige da Fice (NIS).

NIS
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Next Post
Tsadar Mai: Ba Gudu Ba Ja Da Baya Kan Zanga-Zanga -NLC

Tsadar Mai: Ba Gudu Ba Ja Da Baya Kan Zanga-Zanga -NLC

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.