ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Reshen Jihar Ribas Ta Kaddamar Da “Operation Tsaron Iyaka”

by yahuzajere
3 years ago
NIS

Kwanturolan Hukumar Kula da Shige da Fice ta Jihar Ribas (NIS) James Sunday, ya yi wa manema labarai karin haske kan fara aikin “Operation Tsaron Iyaka” a Jihar Ribas.

Kwanturolan ya ce hakan ya samo asali ne daga ganawar da suka yi a jihar Akwa Ibom da mukaddashiyar kwanturola Janar ta Hukumar Shige da Fice, Caroline Wuraola Adepoju wadda ta kai ziyarar aiki ta kwanaki 2 a Akwa Ibom kuma ta ziyarci ofishin kula da iyakoki na ruwa a jihar.
Sauran manyan jami’ai masu mukamin Kwanturola na Shiyyar E na Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya na cikin tawagarta, musamman Kwanturola Akwa Ibom, Abia, Cross River, Ebonyi, Rivers da na Sashen Kula da Iyaka ta Ruwa da ke Jihar Akwa Ibom.

  • “Da Mijina Ya Yi Min Kishiya, Gwamma Ya Rika Kwanciya Da ‘Ya`yanmu”

An yi ziyarar ce domin tantance ayyukan bakin iyaka, ayyuka da ayyukan tattalin arziki da aka gudanar a jihar Rivers kasancewar jihar a gabar ruwa.

ADVERTISEMENT

Kwanturola James Sunday, ya ce “Operation Tsaron Iyaka” wanda ke nuni da karfafa tsaron kan iyaka shi ne abin da zai fi mayar da hankali a kai sakamakon taron da suka yi da kuma amfani da umarnin da mukaddashiyar Kwanturola Janar ta Hukumar Kula da Shige da Fice Caroline Wuraola Adepoju ta bayar, shi ya sa na yanke shawarar fara aikin tare da jami’anmu a Jihar Ribas.

“Jami’amu za su kai samame a wurare da maboya da tashar jiragen ruwa inda ake zargin ‘yan kasar waje da suka shigo Nijeriya ba bisa ka’ida ba suna boye a nan, tare da cafke su da gurfanar da duk wani mutum ko rukuni na bakin haure da aka gano suna zaune ba tare da ingantattun takardu na shigowa ba.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

“Za mu bazama aiki a wannan yunkuri na kawar da ‘yan ci-rani ba bisa ka’ida ba a Jihar Ribas wadanda za su iya shiga aikata cikin munanan ayyuka tare da gujewa gano su a duk lokacin da suka aikata wani laifi ko kuma suka shiga cikin wani abu mara kyau wanda na iya kaiwa ga rashin tsaro ga rayuwa da dukiyoyin mutane a Ribas.” In ji shi.

Sanarwar manema labarai da jami’in hulda da jama’a na reshen hukumar ta NIS da ke JIhar Ribas, ASI Nwosu Chukwu ya fitar, ta kara da cewa hukumar ta fara aiki nan take, kuma za ta ci gaba da aiki har sai ta gamsu da cewa ‘yan ci-rani ba bisa ka’ida ba sun tafi da kansu wuraren da suka kamata domin tsara takardunsu da kuma al’ummarsu ta bin ka’idar ECOWAS da sauran su, da aka shimfida bisa tanade-tanade na Dokar Shige da Fice ta 2015 da Dokokin 2017 da sauran manyan dokokin kasar.

Kwanturola James ya ba da tabbacin masu bin doka da oda daa cikin ‘yan ci-ranin a kullum suna ba su kariya da harkokin kasuwancinsu da rayuwarsu da dukiyoyinsu a Ribas sannan ya shawarci al’umma ko shugabannin kungiyoyi da su fito da jerin sunayen mambobinsu na jihar Ribas domin tabbatar da cewa kowa ya yi rajistar da ta kamata a hukumar ta Shige da Fice (NIS).

NIS
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Tsadar Mai: Ba Gudu Ba Ja Da Baya Kan Zanga-Zanga -NLC

Tsadar Mai: Ba Gudu Ba Ja Da Baya Kan Zanga-Zanga -NLC

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.