• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ECOWAS Ta Bada Umarnin Daukar Matakin Soji A Kan Gwamnatin Nijar

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai, Da ɗumi-ɗuminsa
0
ECOWAS Ta Bada Umarnin Daukar Matakin Soji A Kan Gwamnatin Nijar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika (ECOWAS), ta umarci rundunar ta da ta dauki mataki da nufin mayar da tsarin mulkin Jamhuriyar Nijar.

ECOWAS, ta bayyana hakan ne a lokacin da ta gabatar da kudurinta dangane da juyin mulkin da aka yi a Nijar a wani taro na musamman da aka gudanar a Abuja ranar Alhamis.

  • Golan Real Madrid Courtois Zai Yi Jinyar Watanni Bayan Samun Rauni
  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Soke “Doka Game Da Taiwan”

Baya ga kiran daukar mataki, ECOWAS ta kuma yi kira ga kungiyar tarayyar Afrika (AU), da kasashen da ta ke hulda da kuma cibiyoyin da abin ya shafa da su goyi bayan kudurin da kungiyar ta dauka.

ECOWAS ta bayyana rashin jin dadinta ganin yadda duk wani yunkurin tattaunawa da gwamnatin mulkin soji a Nijar ya ci tura.

Bugu da kari, ECOWAS ta yi kakkausar suka ga ci gaba da tsare shugaba Mohamed Bazoum da ‘yan uwansa.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

“Hukumar ta yi la’akari da takardar da shugaban ECOWAS ya gabatar kan halin da ake ciki a Jamhuriyar Nijar, da kuma yadda ECOWAS ta shiga tsakani tun bayan babban taronta na karshe;

“kuma mun yin la’akari da rahotannin wakilan Nijar da sauran wurare daban-daban;

“Mun yi la’akari da rahoto da shawarwarin kwamitin hafsoshin tsaro na ECOWAS;

“Mun tattauna kan sabon ci gaban da aka samu a Nijar tun bayan babban taron koli na karshe da aka gudanar a ranar 30 ga Yuli, 2023.

“An yi la’akari da cewa, duk kokarin diflomasiyya da ECOWAS ta yi, wajen magance rikicin, shugabannin sojin Jamhuriyar Nijar sun yi watsi da su.

“Sakamakon cikar wa’adin mako guda da aka bayar na mayar da tsarin mulki a Jamhuriyar Nijar mun yake wannan shawara.

“ECOWAS ta nanata kakkausar suka ga juyin mulki da kuma ci gaba da tsare Shugaba Mohammed Bazoam da iyalansa da kuma mambobin gwamnatinsa ba bisa ka’ida ba.

“Kaddamar da kudurin hukumar ECOWAS na warware rikicin.

“Tabbatar da duk matakai musamman na rufe kan iyakoki da tsauraran dokar hana tafiye-tafiye a kan duk mutane ko kungiyoyin mutanen da ayyukansu ke kawo cikas ga duk kokarin da ake na zaman lafiya da nufin tabbatar da ingantaccen tsarin mayar da tsarin mulki.

“Mun gargadi kasashe ta hanyar kawo cikas wajen warware rikicin Nijar cikin lumana game da illar matakin da suka dauka a gaban al’umma.

“Kira ga kungiyar Tarayyar Afirka da ta amince da duk shawarar da hukumar ECOWAS ta dauka kan halin da ake ciki a Nijar.

“Dukkanin kasashe da cibiyoyin hadin gwiwa ciki har da Majalisar Dinkin Duniya da su tallafa wa kungiyar ECOWAS, a kokarinta na tabbatar da mayar da tsarin mulkin kasar cikin gaggawa.”

ECOWAS ta jadadda aniyarta na tabbatar da mulkin dimokuradyya a Jamhuriyar Nijar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BazoumECOWASJuyin MulkiNijarSojojiTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Golan Real Madrid Courtois Zai Yi Jinyar Watanni Bayan Samun Rauni

Next Post

NSCDC Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 10, Ta Kafa ‘Yan Sintiri

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

4 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

20 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

1 day ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

1 day ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

1 day ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Next Post
NSCDC Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 10, Ta Kafa ‘Yan Sintiri

NSCDC Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 10, Ta Kafa 'Yan Sintiri

LABARAI MASU NASABA

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.