ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ECOWAS Ta Bada Umarnin Daukar Matakin Soji A Kan Gwamnatin Nijar

by Sadiq
3 years ago
ECOWAS

Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika (ECOWAS), ta umarci rundunar ta da ta dauki mataki da nufin mayar da tsarin mulkin Jamhuriyar Nijar.

ECOWAS, ta bayyana hakan ne a lokacin da ta gabatar da kudurinta dangane da juyin mulkin da aka yi a Nijar a wani taro na musamman da aka gudanar a Abuja ranar Alhamis.

  • Golan Real Madrid Courtois Zai Yi Jinyar Watanni Bayan Samun Rauni
  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Soke “Doka Game Da Taiwan”

Baya ga kiran daukar mataki, ECOWAS ta kuma yi kira ga kungiyar tarayyar Afrika (AU), da kasashen da ta ke hulda da kuma cibiyoyin da abin ya shafa da su goyi bayan kudurin da kungiyar ta dauka.

ADVERTISEMENT

ECOWAS ta bayyana rashin jin dadinta ganin yadda duk wani yunkurin tattaunawa da gwamnatin mulkin soji a Nijar ya ci tura.

Bugu da kari, ECOWAS ta yi kakkausar suka ga ci gaba da tsare shugaba Mohamed Bazoum da ‘yan uwansa.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

“Hukumar ta yi la’akari da takardar da shugaban ECOWAS ya gabatar kan halin da ake ciki a Jamhuriyar Nijar, da kuma yadda ECOWAS ta shiga tsakani tun bayan babban taronta na karshe;

“kuma mun yin la’akari da rahotannin wakilan Nijar da sauran wurare daban-daban;

“Mun yi la’akari da rahoto da shawarwarin kwamitin hafsoshin tsaro na ECOWAS;

“Mun tattauna kan sabon ci gaban da aka samu a Nijar tun bayan babban taron koli na karshe da aka gudanar a ranar 30 ga Yuli, 2023.

“An yi la’akari da cewa, duk kokarin diflomasiyya da ECOWAS ta yi, wajen magance rikicin, shugabannin sojin Jamhuriyar Nijar sun yi watsi da su.

“Sakamakon cikar wa’adin mako guda da aka bayar na mayar da tsarin mulki a Jamhuriyar Nijar mun yake wannan shawara.

“ECOWAS ta nanata kakkausar suka ga juyin mulki da kuma ci gaba da tsare Shugaba Mohammed Bazoam da iyalansa da kuma mambobin gwamnatinsa ba bisa ka’ida ba.

“Kaddamar da kudurin hukumar ECOWAS na warware rikicin.

“Tabbatar da duk matakai musamman na rufe kan iyakoki da tsauraran dokar hana tafiye-tafiye a kan duk mutane ko kungiyoyin mutanen da ayyukansu ke kawo cikas ga duk kokarin da ake na zaman lafiya da nufin tabbatar da ingantaccen tsarin mayar da tsarin mulki.

“Mun gargadi kasashe ta hanyar kawo cikas wajen warware rikicin Nijar cikin lumana game da illar matakin da suka dauka a gaban al’umma.

“Kira ga kungiyar Tarayyar Afirka da ta amince da duk shawarar da hukumar ECOWAS ta dauka kan halin da ake ciki a Nijar.

“Dukkanin kasashe da cibiyoyin hadin gwiwa ciki har da Majalisar Dinkin Duniya da su tallafa wa kungiyar ECOWAS, a kokarinta na tabbatar da mayar da tsarin mulkin kasar cikin gaggawa.”

ECOWAS ta jadadda aniyarta na tabbatar da mulkin dimokuradyya a Jamhuriyar Nijar.

MASU ALAKA

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi
Manyan Labarai

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

July 7, 2026
Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci
Manyan Labarai

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

July 7, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz
Manyan Labarai

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Next Post
NSCDC Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 10, Ta Kafa ‘Yan Sintiri

NSCDC Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 10, Ta Kafa 'Yan Sintiri

LABARAI MASU NASABA

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

July 7, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

July 7, 2026
'yansanda

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

July 7, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.