ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ECOWAS Ta Bada Umarnin Daukar Matakin Soji A Kan Gwamnatin Nijar

by Sadiq
3 years ago
ECOWAS

Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika (ECOWAS), ta umarci rundunar ta da ta dauki mataki da nufin mayar da tsarin mulkin Jamhuriyar Nijar.

ECOWAS, ta bayyana hakan ne a lokacin da ta gabatar da kudurinta dangane da juyin mulkin da aka yi a Nijar a wani taro na musamman da aka gudanar a Abuja ranar Alhamis.

  • Golan Real Madrid Courtois Zai Yi Jinyar Watanni Bayan Samun Rauni
  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Soke “Doka Game Da Taiwan”

Baya ga kiran daukar mataki, ECOWAS ta kuma yi kira ga kungiyar tarayyar Afrika (AU), da kasashen da ta ke hulda da kuma cibiyoyin da abin ya shafa da su goyi bayan kudurin da kungiyar ta dauka.

ADVERTISEMENT

ECOWAS ta bayyana rashin jin dadinta ganin yadda duk wani yunkurin tattaunawa da gwamnatin mulkin soji a Nijar ya ci tura.

Bugu da kari, ECOWAS ta yi kakkausar suka ga ci gaba da tsare shugaba Mohamed Bazoum da ‘yan uwansa.

LABARAI MASU NASABA

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

“Hukumar ta yi la’akari da takardar da shugaban ECOWAS ya gabatar kan halin da ake ciki a Jamhuriyar Nijar, da kuma yadda ECOWAS ta shiga tsakani tun bayan babban taronta na karshe;

“kuma mun yin la’akari da rahotannin wakilan Nijar da sauran wurare daban-daban;

“Mun yi la’akari da rahoto da shawarwarin kwamitin hafsoshin tsaro na ECOWAS;

“Mun tattauna kan sabon ci gaban da aka samu a Nijar tun bayan babban taron koli na karshe da aka gudanar a ranar 30 ga Yuli, 2023.

“An yi la’akari da cewa, duk kokarin diflomasiyya da ECOWAS ta yi, wajen magance rikicin, shugabannin sojin Jamhuriyar Nijar sun yi watsi da su.

“Sakamakon cikar wa’adin mako guda da aka bayar na mayar da tsarin mulki a Jamhuriyar Nijar mun yake wannan shawara.

“ECOWAS ta nanata kakkausar suka ga juyin mulki da kuma ci gaba da tsare Shugaba Mohammed Bazoam da iyalansa da kuma mambobin gwamnatinsa ba bisa ka’ida ba.

“Kaddamar da kudurin hukumar ECOWAS na warware rikicin.

“Tabbatar da duk matakai musamman na rufe kan iyakoki da tsauraran dokar hana tafiye-tafiye a kan duk mutane ko kungiyoyin mutanen da ayyukansu ke kawo cikas ga duk kokarin da ake na zaman lafiya da nufin tabbatar da ingantaccen tsarin mayar da tsarin mulki.

“Mun gargadi kasashe ta hanyar kawo cikas wajen warware rikicin Nijar cikin lumana game da illar matakin da suka dauka a gaban al’umma.

“Kira ga kungiyar Tarayyar Afirka da ta amince da duk shawarar da hukumar ECOWAS ta dauka kan halin da ake ciki a Nijar.

“Dukkanin kasashe da cibiyoyin hadin gwiwa ciki har da Majalisar Dinkin Duniya da su tallafa wa kungiyar ECOWAS, a kokarinta na tabbatar da mayar da tsarin mulkin kasar cikin gaggawa.”

ECOWAS ta jadadda aniyarta na tabbatar da mulkin dimokuradyya a Jamhuriyar Nijar.

MASU ALAKA

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi
Manyan Labarai

Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

June 13, 2026
Next Post
NSCDC Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 10, Ta Kafa ‘Yan Sintiri

NSCDC Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 10, Ta Kafa 'Yan Sintiri

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.