• English
  • Business News
Monday, September 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwamitin Majalisa Ya Himmatu Wajen Kammala Hanyar Abuja- Kaduna Zuwa Kano

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
2 years ago
in Labarai
0
Kwamitin Majalisa Ya Himmatu Wajen Kammala Hanyar Abuja- Kaduna Zuwa Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamitin Majalisar Wakilai na wucin- gadi kan binciken dalilin tsaikon da aka samu wajen kammala tagwayen hanyar mota kilomita 375 daga Abuja- Kaduna- Kano ya fara gudanar da aikinsa tare da alwashin ganin an kammala aikin cikin lokaci.

Shugaban kwamitin na wucin-gadi, Hon. Abdussamad Dasuki ya bayyana cewar ko kadan ba su da manufar bita- da- kulli ga kowa a binciken illa domin shawo kan kalubalen da ke akwai na tsaikon kammala hanyar wadda Gwamnatin Tarayya ta sake bayar da kwangilar shimfidawa a 2020.

  • Gwamnatin Kaduna Za Ta Yi Bincike Kan Ruftawar Masallacin Fadar Zazzau
  • Majalisar Dokokin Kaduna Ta Amince Da Kwamishinoni 13

Hon. Dasuki wanda ya jagoranci manbobin kwamitin a ziyarar gani da ido a babbar muhimmiyar hanyar, ya kuma bayyana cewar binciken na da manufar ganin an aiwatar da dukkanin sharuda da ka’idojin da aka shata a kwangilar.

LEADERSHIP Hausa ta labarto cewar a yayin rangadin, kwamitin karara ya nuna rashin gamsuwa kan yadda akin ke tafiya da nuna damuwa kan yiyuwar kammala aikin a sabon wa’adin 2025 da Ma’aikatar Ayyuka ta ayyana.

Tun da farko, kwamitin ya gayyaci kamfanin Julius Berger da ke aiwatar da kwangilar da jami’an Ma’aikatar Ayyuka domin jin ta bakin su kan dalilin da yasa duk da makuddan kudaden da aka fitar kan aikin, amma aikin yana nesa ga wa’adin kammalawa. Jami’in kamfanin ya bayyana cewar aikin ya samu tsaiko ne a dalilin rashin tsaro da ke akwai a hanyar.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

A zaman tattaunawa da jami’an Ma’aikatar Ayyuka da kwamitin ya gudanar a karkashin jagorancin Hon. Dasuki, Babbar Sakataren Ma’aikatar, Mamuda Mamman ya bayyanawa kwamitin cewar an kusa kammala aikin sashe na 2 da na 3 na hanyar.

Ya bayyana cewar aikin hanyar a sashen Abuja- Kaduna ya fuskanci matsalar aiwatarwa ta kudi da matsalolin tsaro. Ya ce kusan kashi 20% ne a ka kammala a sashe na 1 daga Abuja zuwa Kaduna, amma ya baiwa kwamitin tabbacin kammala aikin a Mayu 2025.

A yanzu haka dai Kwamitin dai na wucin-gadi yana ci-gaba da aiwatar da aikinsa tare da tsammanin kai rahoto ga Majalisar Wakilai a cikin wa’adin makwanni hudu da majalisa ta baiwa kwamitin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbujaAikiHanyaKadunakano
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Dace Nijeriya Ta Bi Sawun Kasashe Masu Shirin Fita Daga Kangin Dalar Amurka

Next Post

Duniya Ba Ta Bukatar Wani Sabon “Yakin Mummuke”

Related

Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai
Labarai

Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

41 minutes ago
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

3 hours ago
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Manyan Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Buƙaci Al’ummar Jihar Kaduna Da Su Yi Rijistar Katin Zaɓe 

4 hours ago
DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu
Manyan Labarai

DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

6 hours ago
PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu
Manyan Labarai

PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu

7 hours ago
Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME
Ilimi

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

8 hours ago
Next Post
Duniya Ba Ta Bukatar Wani Sabon “Yakin Mummuke”

Duniya Ba Ta Bukatar Wani Sabon “Yakin Mummuke”

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

September 8, 2025
Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

September 8, 2025
Abuja

Jarin Da Sin Ta Zuba Kai Tsaye A Kasashe Cikin Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ya Karu Da Kashi 22.9% A 2024

September 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

September 8, 2025
Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

September 8, 2025
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Buƙaci Al’ummar Jihar Kaduna Da Su Yi Rijistar Katin Zaɓe 

September 8, 2025
Xi Ya Halarci Taron Kungiyar BRICS Ta Yanar Gizo

Xi Ya Halarci Taron Kungiyar BRICS Ta Yanar Gizo

September 8, 2025
DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

September 8, 2025
PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu

PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu

September 8, 2025
Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

September 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.