• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duniya Ba Ta Bukatar Wani Sabon “Yakin Mummuke”

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Duniya Ba Ta Bukatar Wani Sabon “Yakin Mummuke”
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun lokacin da gwamnatin Joe Biden ya fitar da rahoton dabarun tsaro na kasa a watan Oktoba 2022, Amurka ta shirya tsauraran matakai don mummuke kasar Sin. Gabar da take yi da kasar Sin na dada ta’azzara, ciki har da rikicin fasaha na baya-bayan nan wanda ake kira “Chip war”. Wannan matakin da Amurka ta dauka na nuni da sabon “Yakin cacar baki”. Wanda fadar Washington ta kaddamar ba tare da shawarar kowa ba. Kuma wannan mataki ya sabawa yadda zamani ke tafiya a yanzu. 

 

Al’umman Amurka na fama da mabanbanta matsaloli a cikin ’yan shekarun nan, musamman tabarbarewar tsarin siyasarta, tsadar rayuwa, korafe-korafe daga al’umma da rashin jituwa tsakanin jam’iyyun siyasar kasar, wadanda su ne ainihin tushen matsaloli da ya kamata ta magance. A maimakon haka, suke ƙoƙarin canza matsin lambar cikin gida da kasar ke fuskanta ta hanyar zuzuta abin da suke kira “barazana daga waje” wato kasar Sin.

  • Hanyar Mota Daga Gabashi Zuwa Yammacin Aljeriya Kyakkyawan Misali Ne Ga Hadin-Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Raya Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

A zahiri kuma, ’yan kasuwan Amurka sun nuna rashin amincewarsu a aikace yadda Amurka ke tafiyar da lamarin. Misali, tun farkon wannan shekara, sashe daga cikin shugabannin shahararrun kamfanoni suke dafifi zuwa kasar Sin don bincika damar hadin gwiwa. Bari mu fara da Starbucks, Sabon Shugaban kamfanin na kasa da kasa Laxman Narasimhan ya shaida girman damar dake akwai a kasuwar Sin. Shugaban Tesla Elon Musk ya bayyana a fili rashin amincewarsa da wannan lakabin da kasashen yamma suka yi wa Sin na “hadari” tare da yanke mu’amala da ita. Shugaban Nvidia Jensen ya ce ba su shirya “raba gari da Sin” saboda ba su da ikon yin haka, kuma kasancewar kasar Sin daya ce tak a duniya. Duk wadannan na nuni da irin muhimmancin kasuwar Sin game da kamanta adalci da tabbatar da moriyar juna.

 

Labarai Masu Nasaba

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Amma ga mutanen Amurkawa, ko da yake yankin Sin da Amurka suna da tazara da juna, akwai dadadden musayar zumunta tsakanin kasashen biyu mai dogon tarihi. Labaru da dama sun kara jadadda wannan matsayi: labarin damisa masu tashi wato “flying Tigers” a lokacin Yaƙin Duniya na II, labarin “Guling Friends” a lardin Fujian dake gabashin Sin da kuma abota tsakanin Sin da Amurka ta “house in Muscatine” a jihar Iowa, da dai sauransu.

 

Tun lokacin barkewar rikicin Ukraine, kasashen Turai suka bi bayan ƙaddamar da takunkumai mabanbanta a kan Rasha, wanda ya koma kansu ya kuma karfafa rikicin makamashi da hauhawar farashin kayayyakin kasashensu. Tun daga wannan lokaci ne kasashen yamma suka fara nazari kan dangantakarsu da kasar Sin. Kwanan baya, shugaban kasar Faransa Emmanuel Mackron ya bayyana adawarsa game da shishigin Nato a yankin Asiya-Pacific. Kasashe Membobin Tarayyar Turai kamar Jamus, Hungary da Serbia sun bayyana a fili cewa ba za su “daina mu’amala” da Sin ba.

 

Muhimmin dalilin takun-saka tsakanin Amurka da Sin yana ta’allaka ne da irin tsarin manufofin Amurka a kan sauran kasashen duniya, wanda yake haifar da rashin jituwa tsakanin kasashen guda biyu. Ita kasar Sin ta fahimci alfanun dake cikin samun nasara tare, a yayin da ita kuma Amurka ta gwammace ta yi babakere.

 

“Duniya tana da girman da za ta dauki ci gaban kowace kasa ba tare da wani ya nuna fifiko ba.” Yayin zantawarsa da sakatare Tony Blinken na gwamnatin Amurka a kwanan baya, shugaban kasar Sin Xi Jinpingy a ce, Sin da Amurka na iya yin hadin gwiwa don samun nasarorin da za su amfanar da daukacin duniya. Hadin gwiwa tsakanin ƙasashen guda biyu masu mafi girman tattalin arzikin duniya zai daidaita zaman lafiyar duniya, tare da ba da gudunmawa ga raya lamurra da manufofin kasashe masu tasowa.

 

Akwai dalilai da dama da za su sanya manyan giwaye biyu su yi zaman jituwa a cikin daji don bunkasuwa jejin da sauran dabbobin dake cikin shi. Ya kamata Amurka ta daina kumfar baki a kan abubuwan da ba su shafe ta ba. Misalin wannan shi ne sakon da ta aike tarayyar Najeriya a makon da ya gabata inda ta bukaci shugabannin Najeriya su yi taka tsantsan da basussukan da take ciyowa daga kasar Sin. Ya kamata Amurka ta maida hankali a kan daidaita matsalolinta na cikin gida saboda a halin yanzu “Duniya ba ta bukatar wani yakin mummuke”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwamitin Majalisa Ya Himmatu Wajen Kammala Hanyar Abuja- Kaduna Zuwa Kano

Next Post

Sin Da Angola Sun Yi Taro Kan Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya

Related

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita
Daga Birnin Sin

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

2 hours ago
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL
Daga Birnin Sin

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

3 hours ago
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori
Daga Birnin Sin

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

4 hours ago
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

6 hours ago
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

7 hours ago
UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba

1 day ago
Next Post
Sin Da Angola Sun Yi Taro Kan Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya

Sin Da Angola Sun Yi Taro Kan Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.