• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Japan Biris Za Ta Yi Da Hakkin Al’ummarta Da Na Makwabtaka?

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Shin Japan Biris Za Ta Yi Da Hakkin Al’ummarta Da Na Makwabtaka?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Abun mamaki da takaici, duk da adawa daga kasashe makwabta har ma da al’ummar kasar da suke zaman mafiya muhimmanci ga kowane kuduri ko manufar gwamnati, har yanzu Japan tana kan bakanta, inda ta sanar a yau Talata cewa, za ta fara zubar da dagwalon nukilya a cikin teku a ranar Alhamis.

Shin Japan ba ta damu da koke da korafin da al’ummarta ke yi ba ne? Al’ummar kasar da kungiyoyi da kamfanonin masunta, sun bayyana matukar adawa da kudurin gwamnatin kasar, amma da alama, al’ummarta ba sa gabanta, illa abun da ta sa a gaba, wanda ka iya illata al’ummar duniya, har ma da toshewa al’ummarta hanyoyinsu na samun kudin shiga.

  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Kalubalanci Japan Da Ta Dakatar Da Shirin Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku

Su ma al’ummar Koriya ta kudu ba a bar su a baya ba wajen yi zanga-zangar adawa da wannan mataki, a matsayinsu na makwabta da suka fi fuskantar barazanar illar matakin Japan, amma gwamnatinsu ta ki goya musu baya. Shin mene ne amfani gwamnati idan ba za ta tsaya ta kare muradun jama’arta ba? Gwamnati ta al’umma ce, kuma gwamnatin da ta cika gwamnati, ita ce mai sanya al’ummarta gaban komai, wannan ma wani darasi da ya kamata Japan ta dauka daga kasa kamar Sin.

Ba al’ummomin wadannan kasashe ba kadai, kuma ba kasar Sin ce kadai take adawa da wannan mataki ba, akwai tarin masana kimiyya da masu rajin kare muhalli da ma tsibiran yankin Fasifik da sauransu, da suka gargadi Japan ta dakatar da kudurin nata, ta kara nazari bisa kimiyya kafin aiwatar da shi, amma sanarwar ta yau, ta nuna cewa Japan ba ta shirya daga kafa ba.

Illar da wannan mataki za ta haifar ga daukacin al’ummar duniya, ya shafe duk wani buri da Japan ke son cimmawa. Haka zalika, Amurka dake ingiza ta, ita ma ba za ta tsira daga mummunar illar da hakan zai haifar ba domin an san cewa, ruwa ba shi da iyaka.

Labarai Masu Nasaba

FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama

Har yanzu lokaci bai korewa Japan na sauraron al’ummarta da sake nazari domin yin abun da ya dace ba. Kuma ya kamata ta san cewa, baya ga al’ummarta, makwabtanta na da hakki a kanta, kuma Amurka dake ingiza ta, ba za ta kawo mata dauki ba idan abubuwa suka lalace. (Faeza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Matar Aure Ta Kashe Dan Kishiyarta Mai Kwana 4 A Duniya A Bauchi

Next Post

Harkar Tsaro Za Ta Bunkasa Nan Da Shekara Guda -Badaru

Related

FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”
Daga Birnin Sin

FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

21 minutes ago
An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama
Daga Birnin Sin

An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama

1 hour ago
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita
Daga Birnin Sin

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

19 hours ago
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL
Daga Birnin Sin

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

20 hours ago
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori
Daga Birnin Sin

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

21 hours ago
Mu’ammalar Al’adu Muhimmin Karfi Ne Na Ciyar Da Bunkasar Wayewar Kan Bil’adama Da Wanzar Da Zaman Lafiyar Duniya
Daga Birnin Sin

Mu’ammalar Al’adu Muhimmin Karfi Ne Na Ciyar Da Bunkasar Wayewar Kan Bil’adama Da Wanzar Da Zaman Lafiyar Duniya

22 hours ago
Next Post
Ba Gaskiya Ba Ne Cewar Muna Kashe Biliyan 196.9 Ga Masu Juna Biyu – Badaru

Harkar Tsaro Za Ta Bunkasa Nan Da Shekara Guda -Badaru

LABARAI MASU NASABA

FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

July 11, 2025
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba

July 11, 2025
Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (2)

Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (2)

July 11, 2025
An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama

An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama

July 11, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Amurka Ta Rage Wa’adin Bizar ‘Yan Nijeriya Zuwa Wata Uku

July 11, 2025
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

July 11, 2025
Jihohi 10 Sun Kinkimo Bashin Naira Biliyan 417 Duk Da Karin Samun Kudaden Shiga

Jihohi 10 Sun Kinkimo Bashin Naira Biliyan 417 Duk Da Karin Samun Kudaden Shiga

July 11, 2025
Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Shirin Ciyar Da Ɗalibai A Makarantun Zamfara

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Shirin Ciyar Da Ɗalibai A Makarantun Zamfara

July 11, 2025
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

Shugabannin Jam’iyyar ADC Na Jihohi 36 Da Abuja Sun Bayyana Goyon Bayansu Ga David Mark

July 11, 2025
Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote

Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.