ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Harkar Tsaro Za Ta Bunkasa Nan Da Shekara Guda -Badaru

by Abubakar Abba
3 years ago
Tsaro

Ministan tsaro Muhammad Abubakar Badaru, ya umarci jami’an tsaro da su gabatar da jadawali da abubuwan da ake bukata domin kawo karshen kalubalen rashin tsaro a fadin kasar nan. 

Kazalika, ya ce, harkar tsaron kasar nan za ta bunkasa a cikin shekara daya.

  • Shin Japan Biris Za Ta Yi Da Hakkin Al’ummarta Da Na Makwabtaka?
  • Gwamnatin Kaduna Za Ta Raba Tallafi Ga Talakawa Sama Da Miliyan Ɗaya

Badaru ya bayyana hakan ne a shalkwatar ma’aikatar tsaro a yayin da ya kama aiki a matsayin sabon ministan tsaro.

ADVERTISEMENT

Ya ce, aikinsa da na karamin ministan tsaro da kuma aikin manyan jami’in tsaro, na cikin tsaka mai wuya idan har ba mu iya kawo karshen kalubalen rashin tsaro a cikin shekara daya ba.

A cewarsa, harkar tsaron a zamansa na ministan za ta bunkasa a daukacin fadin kasar nan a cikin shekara daya.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Ya ci gaba da cewa, ba mu da wata hujja ta gazawa a kan nauyin da shugaban kasa ya dora mana, inda ya ce, za mu yi iya kokarinmu wajen tsamo kasar nan daga kalubalen rashin tsaro.

Ya kara da cewa, a matsayinmu na ‘yan siyasa ba za mu jurewa gazawa ba, domin zai yi wuya a ce mun gaza, domin ba za mu yadda da gazawa a wannan lokacin ba.

Bugu da kari, Badaru ya yi alkawarin hada kai da daukacin manyan jami’an tsaro a duk wata, domin a hada karfi da karfe wajen kawo karshen kalubalen rashin a kasar nan.

“Na aminta da daukacin matakan da karamin ministan tsaro ya bayyana, amma a nawa bangaren a yau shi ne za kara jaddada kokarinmu da kuma daukar alkawarin cewa, za mu samar da sauyi a fasalin harkar tsaro na kasar nan.”

Kazalika ya ce, “Zamu kuma bai wa daukacin hukumomin tsaro na kasar nan hadin kai kuma nan ba da jimawa ba, za mu fara gudanar da ganawa da hukumomin tsaro a duk wata bisa nufin lalubo da mafita a kan kalubalen rashin tsaro a kasar nan.”

“Mun yi sa’a shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da kansa ya nada manyan jami’an tsaron kuma ya nada mu a matsayin ministocinsa.”

Bugu da kari, ya yi alkawarin yin nazari a kan rahotannin kalubalen rashin tsaro na kasar nan domin a fito da dabarun yadda za a kawo karshen kalubalen rashin tsaro a kasar.

Ya ce, rahotannin na kalubalen rashin tsaron, na nan a ajiye wadanda za su ba mu damar daukar matakan da suka kamata don lalubo da mafita kan matsalar.

A na sa jawabin Hafsan rundunar tsaro Janar Christopher Musa, ya yi alkawarin dawo da zaman lafiya a fadin kasar nan, inda kuma ya yi fatan yaran da ke a kasar nan, za su girma a cikin yanayi na tsaro.

Tsaro
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
An Gudanar Da Bikin Gabatar Da Littafin “Gwagwarmayar Yaki Da Talauci” Cikin Harshen Hausa A Abuja

An Gudanar Da Bikin Gabatar Da Littafin “Gwagwarmayar Yaki Da Talauci” Cikin Harshen Hausa A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.