ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Harkar Tsaro Za Ta Bunkasa Nan Da Shekara Guda -Badaru

by Abubakar Abba
3 years ago
Tsaro

Ministan tsaro Muhammad Abubakar Badaru, ya umarci jami’an tsaro da su gabatar da jadawali da abubuwan da ake bukata domin kawo karshen kalubalen rashin tsaro a fadin kasar nan. 

Kazalika, ya ce, harkar tsaron kasar nan za ta bunkasa a cikin shekara daya.

  • Shin Japan Biris Za Ta Yi Da Hakkin Al’ummarta Da Na Makwabtaka?
  • Gwamnatin Kaduna Za Ta Raba Tallafi Ga Talakawa Sama Da Miliyan Ɗaya

Badaru ya bayyana hakan ne a shalkwatar ma’aikatar tsaro a yayin da ya kama aiki a matsayin sabon ministan tsaro.

ADVERTISEMENT

Ya ce, aikinsa da na karamin ministan tsaro da kuma aikin manyan jami’in tsaro, na cikin tsaka mai wuya idan har ba mu iya kawo karshen kalubalen rashin tsaro a cikin shekara daya ba.

A cewarsa, harkar tsaron a zamansa na ministan za ta bunkasa a daukacin fadin kasar nan a cikin shekara daya.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Ya ci gaba da cewa, ba mu da wata hujja ta gazawa a kan nauyin da shugaban kasa ya dora mana, inda ya ce, za mu yi iya kokarinmu wajen tsamo kasar nan daga kalubalen rashin tsaro.

Ya kara da cewa, a matsayinmu na ‘yan siyasa ba za mu jurewa gazawa ba, domin zai yi wuya a ce mun gaza, domin ba za mu yadda da gazawa a wannan lokacin ba.

Bugu da kari, Badaru ya yi alkawarin hada kai da daukacin manyan jami’an tsaro a duk wata, domin a hada karfi da karfe wajen kawo karshen kalubalen rashin a kasar nan.

“Na aminta da daukacin matakan da karamin ministan tsaro ya bayyana, amma a nawa bangaren a yau shi ne za kara jaddada kokarinmu da kuma daukar alkawarin cewa, za mu samar da sauyi a fasalin harkar tsaro na kasar nan.”

Kazalika ya ce, “Zamu kuma bai wa daukacin hukumomin tsaro na kasar nan hadin kai kuma nan ba da jimawa ba, za mu fara gudanar da ganawa da hukumomin tsaro a duk wata bisa nufin lalubo da mafita a kan kalubalen rashin tsaro a kasar nan.”

“Mun yi sa’a shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da kansa ya nada manyan jami’an tsaron kuma ya nada mu a matsayin ministocinsa.”

Bugu da kari, ya yi alkawarin yin nazari a kan rahotannin kalubalen rashin tsaro na kasar nan domin a fito da dabarun yadda za a kawo karshen kalubalen rashin tsaro a kasar.

Ya ce, rahotannin na kalubalen rashin tsaron, na nan a ajiye wadanda za su ba mu damar daukar matakan da suka kamata don lalubo da mafita kan matsalar.

A na sa jawabin Hafsan rundunar tsaro Janar Christopher Musa, ya yi alkawarin dawo da zaman lafiya a fadin kasar nan, inda kuma ya yi fatan yaran da ke a kasar nan, za su girma a cikin yanayi na tsaro.

Tsaro
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Next Post
An Gudanar Da Bikin Gabatar Da Littafin “Gwagwarmayar Yaki Da Talauci” Cikin Harshen Hausa A Abuja

An Gudanar Da Bikin Gabatar Da Littafin “Gwagwarmayar Yaki Da Talauci” Cikin Harshen Hausa A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.