• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Karrama Xi Da Lambar Yabo Ta Afirka Ta Kudu, Sannan Xi da Cyril Ramaphosa Sun Gana Da ’Yan Jaridu

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
An Karrama Xi Da Lambar Yabo Ta Afirka Ta Kudu, Sannan Xi da Cyril Ramaphosa Sun Gana Da ’Yan Jaridu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Talatar nan ne shugaban kasar Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa, ya karrama takwaransa na kasar Sin Xi Jinping da lambar yabo ta Afirka ta Kudu.

Da yake jawabi a wajen bikin, Xi ya ce, dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare dake tsakanin Sin da Afirka ta Kudu ta shiga muhimmin lokaci, yayin da amincewa da juna ta fuskar siyasa ke ci gaba da zurfafa, kuma hadin gwiwar moriyar juna a aikace a fannoni daban-daban ta haifar da sakamako mai gamsarwa.

  • Shin Japan Biris Za Ta Yi Da Hakkin Al’ummarta Da Na Makwabtaka?

Ya kara da cewa, kasashen biyu sun ci gaba da yin hadin gwiwa a harkoki na kasa da kasa, wanda ya taimaka wajen ci gaba da ma farfadowarsu, tare da ba da gagarumar gudummawa wajen kiyaye moriyar kasashe masu tasowa.

Ya kuma bayyana cewa, zai martaba wannan karramawa, wadda ke nuna alakar abokantaka a tsakanin al’ummomin kasashen biyu, Xi ya kuma yi alkawarin kara himmantuwa wajen ci gaba da raya dangantakar dake tsakanin Sin da Afirka ta Kudu.

Sannan a yammacin yau Talatar nan ne shugaba Xi Jinping na kasar Sin da takwaransa na kasar Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa suka gana da manema labaru bayan shawarwarin da suka yi a fadar shugaban Afirka ta Kudu da ke birnin Pretoria.

Labarai Masu Nasaba

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

Xi ya bayyana cewa, a bana aka cika shekaru 25 da kulla huldar diplomasiyya a tsakanin Sin da Afirka ta Kudu. Dangantakar dake tsakanin Sin da Afirka ta Kudu ta samu ci gaba mai zurfi a cikin shekaru 25 da suka gabata, inda amincewa da juna bisa manyan tsare-tsare ya kai wani sabon matsayi.

Haka kuma dangantakar da ke tsakanin Sin da Afirka ta Kudu ta zarce alakar sassan biyu, har ma ta yi tasiri a duniya. Dazun nan shugaba Ramaphosa da Xi sun yi shawarwari a tsakaninsu, inda suka yi musayar ra’ayoyi dangane da ci gaban huldar da ke tsakanin kasashen 2 a sabon zamani da kuma al’amuran kasa da kasa da na shiyya-shiyya wadanda suka jawo hankalinsu duka, tare da cimma daidaito mai muhimmanci.

A nasa bangaren, shugaba Ramaphosa ya ce, dukkan shugabannin 2 sun amince da zurfafa hadin gwiwar kasashen 2 a fannonin ciniki da zuba jari, da fadada hadin kan moriyar juna a fannonin ababen more rayuwar jama’a, yawon bude ido, ba da ilmi, tattalin arziki na zamani da dai sauransu, tare da kara taimakawa juna a manyan al’amuran kasa da kasa da na shiyya-shiyya. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Bukaci Japan Da Ta Dakatar Da Mummunar Shawarar Da Ta Yanke Ta Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku

Next Post

Rikici Ya Kaure Tsakanin ‘Yan Bindiga A Benuwe, Sun Fara Kashe Juna

Related

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu
Daga Birnin Sin

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

2 hours ago
Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU
Daga Birnin Sin

Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

3 hours ago
Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana
Daga Birnin Sin

Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

4 hours ago
Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”
Daga Birnin Sin

Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

5 hours ago
Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

6 hours ago
PLA Ta Kori Jirgin Ruwan Yakin Amurka Daga Yankin Ruwan Kasar Sin A Kusa Da Huangyan Dao
Daga Birnin Sin

PLA Ta Kori Jirgin Ruwan Yakin Amurka Daga Yankin Ruwan Kasar Sin A Kusa Da Huangyan Dao

7 hours ago
Next Post
Rikici Ya Kaure Tsakanin ‘Yan Bindiga A Benuwe, Sun Fara Kashe Juna

Rikici Ya Kaure Tsakanin 'Yan Bindiga A Benuwe, Sun Fara Kashe Juna

LABARAI MASU NASABA

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

August 13, 2025
Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

August 13, 2025
APC

2027: Jagororin APC Na Kudu-maso-Yamma Sun Amince Da Tinubu Ya Sake Tsayawa Takara

August 13, 2025
Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

August 13, 2025
Tinubu

Rangwame: Tinubu Ya Bada Umarnin Sake Bitar Tsarin Yadda Ake Karɓar Haraji 

August 13, 2025
Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

August 13, 2025
Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

August 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

August 13, 2025
Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

August 13, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati

August 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.