ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, September 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Karrama Xi Da Lambar Yabo Ta Afirka Ta Kudu, Sannan Xi da Cyril Ramaphosa Sun Gana Da ’Yan Jaridu

by CMG Hausa
3 years ago
Xi

Talatar nan ne shugaban kasar Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa, ya karrama takwaransa na kasar Sin Xi Jinping da lambar yabo ta Afirka ta Kudu.

Da yake jawabi a wajen bikin, Xi ya ce, dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare dake tsakanin Sin da Afirka ta Kudu ta shiga muhimmin lokaci, yayin da amincewa da juna ta fuskar siyasa ke ci gaba da zurfafa, kuma hadin gwiwar moriyar juna a aikace a fannoni daban-daban ta haifar da sakamako mai gamsarwa.

  • Shin Japan Biris Za Ta Yi Da Hakkin Al’ummarta Da Na Makwabtaka?

Ya kara da cewa, kasashen biyu sun ci gaba da yin hadin gwiwa a harkoki na kasa da kasa, wanda ya taimaka wajen ci gaba da ma farfadowarsu, tare da ba da gagarumar gudummawa wajen kiyaye moriyar kasashe masu tasowa.

ADVERTISEMENT

Ya kuma bayyana cewa, zai martaba wannan karramawa, wadda ke nuna alakar abokantaka a tsakanin al’ummomin kasashen biyu, Xi ya kuma yi alkawarin kara himmantuwa wajen ci gaba da raya dangantakar dake tsakanin Sin da Afirka ta Kudu.

Sannan a yammacin yau Talatar nan ne shugaba Xi Jinping na kasar Sin da takwaransa na kasar Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa suka gana da manema labaru bayan shawarwarin da suka yi a fadar shugaban Afirka ta Kudu da ke birnin Pretoria.

LABARAI MASU NASABA

CIFTIS Ya Zurfafa Cimma Matsaya Kan Hadin Gwiwar Duniya A Fannin Hidimomi

Shugabannin BRICS Sun Amince Da Sanarwar Hadin Gwiwa A Taron Koli Na New Delhi

Xi ya bayyana cewa, a bana aka cika shekaru 25 da kulla huldar diplomasiyya a tsakanin Sin da Afirka ta Kudu. Dangantakar dake tsakanin Sin da Afirka ta Kudu ta samu ci gaba mai zurfi a cikin shekaru 25 da suka gabata, inda amincewa da juna bisa manyan tsare-tsare ya kai wani sabon matsayi.

Haka kuma dangantakar da ke tsakanin Sin da Afirka ta Kudu ta zarce alakar sassan biyu, har ma ta yi tasiri a duniya. Dazun nan shugaba Ramaphosa da Xi sun yi shawarwari a tsakaninsu, inda suka yi musayar ra’ayoyi dangane da ci gaban huldar da ke tsakanin kasashen 2 a sabon zamani da kuma al’amuran kasa da kasa da na shiyya-shiyya wadanda suka jawo hankalinsu duka, tare da cimma daidaito mai muhimmanci.

A nasa bangaren, shugaba Ramaphosa ya ce, dukkan shugabannin 2 sun amince da zurfafa hadin gwiwar kasashen 2 a fannonin ciniki da zuba jari, da fadada hadin kan moriyar juna a fannonin ababen more rayuwar jama’a, yawon bude ido, ba da ilmi, tattalin arziki na zamani da dai sauransu, tare da kara taimakawa juna a manyan al’amuran kasa da kasa da na shiyya-shiyya. (Ibrahim Yaya)

Xi
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

CIFTIS Ya Zurfafa Cimma Matsaya Kan Hadin Gwiwar Duniya A Fannin Hidimomi
Daga Birnin Sin

CIFTIS Ya Zurfafa Cimma Matsaya Kan Hadin Gwiwar Duniya A Fannin Hidimomi

September 14, 2026
Shugabannin BRICS Sun Amince Da Sanarwar Hadin Gwiwa A Taron Koli Na New Delhi
Daga Birnin Sin

Shugabannin BRICS Sun Amince Da Sanarwar Hadin Gwiwa A Taron Koli Na New Delhi

September 13, 2026
Ministan Kimiyya Na Afirka Ta Kudu Ya Yi Kiran Zurfafa Hadin Gwiwar Kimiyya Da Fasaha Da Sin
Daga Birnin Sin

Ministan Kimiyya Na Afirka Ta Kudu Ya Yi Kiran Zurfafa Hadin Gwiwar Kimiyya Da Fasaha Da Sin

September 13, 2026
Next Post
Rikici Ya Kaure Tsakanin ‘Yan Bindiga A Benuwe, Sun Fara Kashe Juna

Rikici Ya Kaure Tsakanin 'Yan Bindiga A Benuwe, Sun Fara Kashe Juna

LABARAI MASU NASABA

Ta’aziyyar Bamanga: Gwamna Fintiri Ya Ayyana Litinin Ranar Hutun Aiki

Ta’aziyyar Bamanga: Gwamna Fintiri Ya Ayyana Litinin Ranar Hutun Aiki

September 14, 2026
Dangote

Matatar Dangote Ta Fara Sayar Da Hannun Jari Na Naira Tiriliyan 2.15

September 14, 2026
Boko Haram Ta Lalata Makarantu 5,000 A Borno – Zulum

Boko Haram Ta Lalata Makarantu 5,000 A Borno – Zulum

September 14, 2026
CIFTIS Ya Zurfafa Cimma Matsaya Kan Hadin Gwiwar Duniya A Fannin Hidimomi

CIFTIS Ya Zurfafa Cimma Matsaya Kan Hadin Gwiwar Duniya A Fannin Hidimomi

September 14, 2026
Dansanda Ya Ki Karbar Cin Hancin Miliyan 1 Kan Ya Saki Wani Barawon Mutane A Kano

Jami’an Tsaro Sun Ƙaddamar Da Aikin Ceto Limaman Da Aka Sace Bayan Taron APC A Zamfara 

September 14, 2026
Manchester Derby: City Ta Nunawa United Kwanji A Old Trafford

Manchester Derby: City Ta Nunawa United Kwanji A Old Trafford

September 13, 2026
Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

September 13, 2026
Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

Makiyaya Sun Yi Asarar Shanu 200,000 Ta Dalilin Rikice-Rikice – MACBAN

September 13, 2026
Xi

Farashin Man Fetur Ya Sake Tashi A Abuja

September 13, 2026
Shugabannin BRICS Sun Amince Da Sanarwar Hadin Gwiwa A Taron Koli Na New Delhi

Shugabannin BRICS Sun Amince Da Sanarwar Hadin Gwiwa A Taron Koli Na New Delhi

September 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.