• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping: Za Kara Karfin Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi Jinping: Za Kara Karfin Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A safiyar yau Alhamis 24 ga wata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya halarci taron manema labaru na musamman na taron kolin BRICS karo na 15 a birnin Johannesburg na kasar Afirka ta kudu.

Taron ya sanar da cewa, an gayyaci Saudiyya, Masar, Hadaddiyar Daular Larabawa, Argentina, Iran, da Habasha don zama mambobin kungiyar BRICS a hukumance.

  • Ciniki Tsakanin Sin Da Afirka Ya Samu Ci Gaba A Watanni 7 Na Farkon Bana

A cikin muhimmin jawabinsa, Xi Jinping ya yi nuni da cewa, kasashen BRICS kasashe ne dake da babban tasiri, da kuma sauke muhimman nauyin da ya rataya a wuyansu na tabbatar da zaman lafiya da ci gaban duniya.

Ya ce, a yayin wannan taro, mun gudanar da tattaunawa mai zurfi kan batutuwan da suka hada da halin da duniya ke ciki, da hadin gwiwar kasashen BRICS, kana mun cimma matsaya guda a fannoni daban daban, da fitar da sanarwar taron koli, ana iya cewa, an cimma nasarori masu yawa.

Baya ga haka, Xi Jinping ya yi nuni da cewa, shugabannin kasashen biyar sun amince da gayyatar kasashen Saudiyya, Masar, Hadaddiyar Daular Larabawa, da Argentina, da Iran da kuma Habasha, don zama mambobin BRICS. Kasar Sin na taya wa wadannan kasashe murna.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Xi Jinping ya jaddada cewa, aikin fadada mambobin BRICS na da ma’ana a tarihi, matakin da ya nuna aniyar kasashen BRICS na hada kai da kasashe masu tasowa, wanda ya dace da fatawar al’ummomin duniya, tare da biyan bukatun bai daya na sabbin kasashen da tattalin arzikinsu ke bunkasa da ma kasashe masu tasowa. Har ila yau, ya kasance wani sabon mafari na hadin gwiwar kasashen BRICS, wanda zai sanya sabbin kuzari a cikin tsarin hadin gwiwar BRICS, da kara karfin tabbatar da zaman lafiya da ci gaban duniya.

Shugaban kasar Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa ne ya jagoranci taron, yayin da shugaban kasar Brazil Luiz Inácio Lula da Silva, da firaministan kasar Indiya Narendra Damodardas Modi da shugaban kasar Rasha Vladimir Putin wanda ya halarci taron ta kafar bidiyo suka halarci taro.

Taron ya kuma amince da fitar da “Sanarwar Johannesburg ta taron kolin BRICS karo an 15”.

A yayin da yake halartar taron tattaunawa tsakanin shugabannin kasashen BRICS, da kasashen Afirka da sauran sabbin kasashen da tattalin arzikinsu ke bunkasa da kasashe masu tasowa a birnin Johannesburg, Xi ya nuna cewa, kasarsa ta riga ta kaddamar da wani asusu na musamman na shirin raya kasa na duniya da hadin kan kasashe masu tasowa, a sa’i daya kuma ya bayyana cewa, a ko da yaushe kasar Sin tana numfasawa kamar kowace kasa tare da raba makoma guda da kasashe masu tasowa, kuma ta kasance, kuma za ta ci gaba da kasancewa mamba a cikinsu har abada. (Mai fassara: Bilkisu Xin)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Dumi-dumi: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Abba Gida-gida Ya Shigar A Gabanta

Next Post

FIFA Ta Fara Bincike Kan Sumbata Da Rubiales Ya Yi Wa ‘Yar Wasan Spain

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

13 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

14 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

16 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

19 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

20 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

21 hours ago
Next Post
FIFA Ta Fara Bincike Kan Sumbata Da Rubiales Ya Yi Wa ‘Yar Wasan Spain

FIFA Ta Fara Bincike Kan Sumbata Da Rubiales Ya Yi Wa 'Yar Wasan Spain

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.