ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping: Za Kara Karfin Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
Jinping

A safiyar yau Alhamis 24 ga wata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya halarci taron manema labaru na musamman na taron kolin BRICS karo na 15 a birnin Johannesburg na kasar Afirka ta kudu.

Taron ya sanar da cewa, an gayyaci Saudiyya, Masar, Hadaddiyar Daular Larabawa, Argentina, Iran, da Habasha don zama mambobin kungiyar BRICS a hukumance.

  • Ciniki Tsakanin Sin Da Afirka Ya Samu Ci Gaba A Watanni 7 Na Farkon Bana

A cikin muhimmin jawabinsa, Xi Jinping ya yi nuni da cewa, kasashen BRICS kasashe ne dake da babban tasiri, da kuma sauke muhimman nauyin da ya rataya a wuyansu na tabbatar da zaman lafiya da ci gaban duniya.

ADVERTISEMENT

Ya ce, a yayin wannan taro, mun gudanar da tattaunawa mai zurfi kan batutuwan da suka hada da halin da duniya ke ciki, da hadin gwiwar kasashen BRICS, kana mun cimma matsaya guda a fannoni daban daban, da fitar da sanarwar taron koli, ana iya cewa, an cimma nasarori masu yawa.

Baya ga haka, Xi Jinping ya yi nuni da cewa, shugabannin kasashen biyar sun amince da gayyatar kasashen Saudiyya, Masar, Hadaddiyar Daular Larabawa, da Argentina, da Iran da kuma Habasha, don zama mambobin BRICS. Kasar Sin na taya wa wadannan kasashe murna.

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Xi Jinping ya jaddada cewa, aikin fadada mambobin BRICS na da ma’ana a tarihi, matakin da ya nuna aniyar kasashen BRICS na hada kai da kasashe masu tasowa, wanda ya dace da fatawar al’ummomin duniya, tare da biyan bukatun bai daya na sabbin kasashen da tattalin arzikinsu ke bunkasa da ma kasashe masu tasowa. Har ila yau, ya kasance wani sabon mafari na hadin gwiwar kasashen BRICS, wanda zai sanya sabbin kuzari a cikin tsarin hadin gwiwar BRICS, da kara karfin tabbatar da zaman lafiya da ci gaban duniya.

Shugaban kasar Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa ne ya jagoranci taron, yayin da shugaban kasar Brazil Luiz Inácio Lula da Silva, da firaministan kasar Indiya Narendra Damodardas Modi da shugaban kasar Rasha Vladimir Putin wanda ya halarci taron ta kafar bidiyo suka halarci taro.

Taron ya kuma amince da fitar da “Sanarwar Johannesburg ta taron kolin BRICS karo an 15”.

A yayin da yake halartar taron tattaunawa tsakanin shugabannin kasashen BRICS, da kasashen Afirka da sauran sabbin kasashen da tattalin arzikinsu ke bunkasa da kasashe masu tasowa a birnin Johannesburg, Xi ya nuna cewa, kasarsa ta riga ta kaddamar da wani asusu na musamman na shirin raya kasa na duniya da hadin kan kasashe masu tasowa, a sa’i daya kuma ya bayyana cewa, a ko da yaushe kasar Sin tana numfasawa kamar kowace kasa tare da raba makoma guda da kasashe masu tasowa, kuma ta kasance, kuma za ta ci gaba da kasancewa mamba a cikinsu har abada. (Mai fassara: Bilkisu Xin)

Jinping
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
Daga Birnin Sin

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Daga Birnin Sin

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Next Post
FIFA Ta Fara Bincike Kan Sumbata Da Rubiales Ya Yi Wa ‘Yar Wasan Spain

FIFA Ta Fara Bincike Kan Sumbata Da Rubiales Ya Yi Wa 'Yar Wasan Spain

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.