ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping: Za Kara Karfin Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
Jinping

A safiyar yau Alhamis 24 ga wata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya halarci taron manema labaru na musamman na taron kolin BRICS karo na 15 a birnin Johannesburg na kasar Afirka ta kudu.

Taron ya sanar da cewa, an gayyaci Saudiyya, Masar, Hadaddiyar Daular Larabawa, Argentina, Iran, da Habasha don zama mambobin kungiyar BRICS a hukumance.

  • Ciniki Tsakanin Sin Da Afirka Ya Samu Ci Gaba A Watanni 7 Na Farkon Bana

A cikin muhimmin jawabinsa, Xi Jinping ya yi nuni da cewa, kasashen BRICS kasashe ne dake da babban tasiri, da kuma sauke muhimman nauyin da ya rataya a wuyansu na tabbatar da zaman lafiya da ci gaban duniya.

ADVERTISEMENT

Ya ce, a yayin wannan taro, mun gudanar da tattaunawa mai zurfi kan batutuwan da suka hada da halin da duniya ke ciki, da hadin gwiwar kasashen BRICS, kana mun cimma matsaya guda a fannoni daban daban, da fitar da sanarwar taron koli, ana iya cewa, an cimma nasarori masu yawa.

Baya ga haka, Xi Jinping ya yi nuni da cewa, shugabannin kasashen biyar sun amince da gayyatar kasashen Saudiyya, Masar, Hadaddiyar Daular Larabawa, da Argentina, da Iran da kuma Habasha, don zama mambobin BRICS. Kasar Sin na taya wa wadannan kasashe murna.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Xi Jinping ya jaddada cewa, aikin fadada mambobin BRICS na da ma’ana a tarihi, matakin da ya nuna aniyar kasashen BRICS na hada kai da kasashe masu tasowa, wanda ya dace da fatawar al’ummomin duniya, tare da biyan bukatun bai daya na sabbin kasashen da tattalin arzikinsu ke bunkasa da ma kasashe masu tasowa. Har ila yau, ya kasance wani sabon mafari na hadin gwiwar kasashen BRICS, wanda zai sanya sabbin kuzari a cikin tsarin hadin gwiwar BRICS, da kara karfin tabbatar da zaman lafiya da ci gaban duniya.

Shugaban kasar Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa ne ya jagoranci taron, yayin da shugaban kasar Brazil Luiz Inácio Lula da Silva, da firaministan kasar Indiya Narendra Damodardas Modi da shugaban kasar Rasha Vladimir Putin wanda ya halarci taron ta kafar bidiyo suka halarci taro.

Taron ya kuma amince da fitar da “Sanarwar Johannesburg ta taron kolin BRICS karo an 15”.

A yayin da yake halartar taron tattaunawa tsakanin shugabannin kasashen BRICS, da kasashen Afirka da sauran sabbin kasashen da tattalin arzikinsu ke bunkasa da kasashe masu tasowa a birnin Johannesburg, Xi ya nuna cewa, kasarsa ta riga ta kaddamar da wani asusu na musamman na shirin raya kasa na duniya da hadin kan kasashe masu tasowa, a sa’i daya kuma ya bayyana cewa, a ko da yaushe kasar Sin tana numfasawa kamar kowace kasa tare da raba makoma guda da kasashe masu tasowa, kuma ta kasance, kuma za ta ci gaba da kasancewa mamba a cikinsu har abada. (Mai fassara: Bilkisu Xin)

Jinping
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
FIFA Ta Fara Bincike Kan Sumbata Da Rubiales Ya Yi Wa ‘Yar Wasan Spain

FIFA Ta Fara Bincike Kan Sumbata Da Rubiales Ya Yi Wa 'Yar Wasan Spain

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.