• English
  • Business News
Saturday, June 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Tabbatar Da Gaskiya Da Adalci -Kwamitin Rabon Abinci A Adamawa

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
in Labarai
0
Za Mu Tabbatar Da Gaskiya Da Adalci -Kwamitin Rabon Abinci A Adamawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamitin da gwamnan jihar Adamawa Ahmadu Umaru Fintiri, ya dora wa alhakin raba kayayyakin abinci da rage radadi, biyo bayan cire tallafin man fetur da gwamnatin tarayya ta yi, ya bayyana tsare-tsaren ganin rabon ya kai ga mutanen da suka fi bukata.

Da yake jawabi jim kadan da kammala ganawar da mambobin kwamitin suka yi a Yola a ranar Litinin, sakataren gwamnatin jihar Awwal Bamanga Tukur, wanda kuma shi ne shugaban kwamitin, ya ce za su tabbatar da gaskiya da adalci a rabon.

  • Mutane Sun Daka Wa Kayan Abinci Wawa A Bayelsa Saboda Yunwa
  • Tinubu Ya Umarci Rage Yawan Masu Zuwa Taron UNGA Don Rage Kashe Kudin Gwamnati 

Ya ci gaba da cewa “shirin zai shafi harkokin jama’a ta kowane bangare, musamman tafiye-tafiye, rage kudaden farashin kayayyakin abinci da kashi 50 bisa dari, a daukacin cibiyoyin kada kuri’a 266, a fadin jihar.

“Shirin zai kawo saukin tafiye-tafiye ga ma’aikata, ‘yan makaranta, masu kananan karfi da matafiya da ke shigowar jiha, kan haka mun samar da motocin bas-bas 10 daga kamfanin Innoson a kan kudi naira biliyan 1.06”.

Tukur, ya ce manufar shirin shi ne kawo sauki ga wahalhalun da jama’a ke ciki, ya ce “mutane mabukata kamar; matan da mazajensu suka mutu, matan da aurensu ya mutu, nakasassun mutane, makarantun kwana da kungiyoyin mata da matasa su za su amfana da shirin, za mu tabbatar kowa ya amfani” in ji Bamanga.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci

Haka kuma sakataren gwamnatin jihar Awwal Tukur, ya ce gwamnatin jihar ta karbi tallafin naira miliyan dubu biyu, daga gwamnatin tarayya, kari kan tirelan biyar na shinkafa, yabce ita ma gwamnatin jihar ta samar da tirela 50, na shinkafa da masara.

“Bisa umarni, za mu tabbatar da jama’a sun samu sauki, za mu tabbatar farashinmu ya karya farashin abinci a kasuwa, za mu sayarda karamin buhu a kan kudi naira dubu 10, ba kamar yadda yake a kasuwa dubu 20 ba” in ji Bamanga.

Shugaban kwamitin ya ce kwamitin yana da masu sa ido game yadda shirin zai ci gaba da gudana, ya roke ‘yan jaridu da su rika bibiyan aikin kwamitn, ana dai tsamammin za a fara aikin a ranar Laraba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutane Sun Daka Wa Kayan Abinci Wawa A Bayelsa Saboda Yunwa

Next Post

Sharuda 5 Da Tinubu Ya Gindaya Wa Ministocinsa

Related

Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai
Labarai

Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai

2 hours ago
DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
Manyan Labarai

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci

3 hours ago
Tinubu
Labarai

Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa

4 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci

5 hours ago
jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

17 hours ago
Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

18 hours ago
Next Post
Sharuda 5 Da Tinubu Ya Gindaya Wa Ministocinsa

Sharuda 5 Da Tinubu Ya Gindaya Wa Ministocinsa

LABARAI MASU NASABA

Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)

Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)

June 14, 2025
Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)

Kula Da Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi

June 14, 2025
Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai

Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai

June 14, 2025
Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su

Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su

June 14, 2025
DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci

June 14, 2025
Tinubu

Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa

June 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci

June 14, 2025
Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

June 14, 2025
Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

June 14, 2025
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

June 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.