ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Tabbatar Da Gaskiya Da Adalci -Kwamitin Rabon Abinci A Adamawa

by Muh'd Shafi'u Saleh
3 years ago
Adamawa

Kwamitin da gwamnan jihar Adamawa Ahmadu Umaru Fintiri, ya dora wa alhakin raba kayayyakin abinci da rage radadi, biyo bayan cire tallafin man fetur da gwamnatin tarayya ta yi, ya bayyana tsare-tsaren ganin rabon ya kai ga mutanen da suka fi bukata.

Da yake jawabi jim kadan da kammala ganawar da mambobin kwamitin suka yi a Yola a ranar Litinin, sakataren gwamnatin jihar Awwal Bamanga Tukur, wanda kuma shi ne shugaban kwamitin, ya ce za su tabbatar da gaskiya da adalci a rabon.

  • Mutane Sun Daka Wa Kayan Abinci Wawa A Bayelsa Saboda Yunwa
  • Tinubu Ya Umarci Rage Yawan Masu Zuwa Taron UNGA Don Rage Kashe Kudin Gwamnati 

Ya ci gaba da cewa “shirin zai shafi harkokin jama’a ta kowane bangare, musamman tafiye-tafiye, rage kudaden farashin kayayyakin abinci da kashi 50 bisa dari, a daukacin cibiyoyin kada kuri’a 266, a fadin jihar.

ADVERTISEMENT

“Shirin zai kawo saukin tafiye-tafiye ga ma’aikata, ‘yan makaranta, masu kananan karfi da matafiya da ke shigowar jiha, kan haka mun samar da motocin bas-bas 10 daga kamfanin Innoson a kan kudi naira biliyan 1.06”.

Tukur, ya ce manufar shirin shi ne kawo sauki ga wahalhalun da jama’a ke ciki, ya ce “mutane mabukata kamar; matan da mazajensu suka mutu, matan da aurensu ya mutu, nakasassun mutane, makarantun kwana da kungiyoyin mata da matasa su za su amfana da shirin, za mu tabbatar kowa ya amfani” in ji Bamanga.

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

Haka kuma sakataren gwamnatin jihar Awwal Tukur, ya ce gwamnatin jihar ta karbi tallafin naira miliyan dubu biyu, daga gwamnatin tarayya, kari kan tirelan biyar na shinkafa, yabce ita ma gwamnatin jihar ta samar da tirela 50, na shinkafa da masara.

“Bisa umarni, za mu tabbatar da jama’a sun samu sauki, za mu tabbatar farashinmu ya karya farashin abinci a kasuwa, za mu sayarda karamin buhu a kan kudi naira dubu 10, ba kamar yadda yake a kasuwa dubu 20 ba” in ji Bamanga.

Shugaban kwamitin ya ce kwamitin yana da masu sa ido game yadda shirin zai ci gaba da gudana, ya roke ‘yan jaridu da su rika bibiyan aikin kwamitn, ana dai tsamammin za a fara aikin a ranar Laraba.

Adamawa
Muh'd Shafi'u Saleh
+ postsBio
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Jami’in Tsaro Ya Mayar da Dala 505 Da Riyal 30 Da Ya Tsinta A Yola
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Shahararren Malamin Addinin Islama A Adamawa Sheikh Ibrahim Abubakar Daware Ya Rasu
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    An Yi Wa ‘Yansanda 110 Ƙarin Girma A Adamawa
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Gwamna Fintiri Ya Nada Sabbin Sarakuna 7 A Jihar Adamawa

MASU ALAKA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
Ra'ayi Riga

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Next Post
Sharuda 5 Da Tinubu Ya Gindaya Wa Ministocinsa

Sharuda 5 Da Tinubu Ya Gindaya Wa Ministocinsa

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.