• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Benin Da Kuma Aika Sakwanni Ga Takwarorinsa na Zimbabwe Da AFirka Ta Kudu

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi Jinping
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da yammacin yau Juma’a ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya tattauna da takwaransa na kasar Benin Patrice Talon, wanda ke ziyarar aiki a nan birnin Beijing, inda bangarorin biyu suka sanar da kafa dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare.

Xi Jinping ya nuna cewa, Sin na goyon bayan nahiyar Afrika, a fannin zama wani muhimmin bangare na siyasa, da tattalin arziki, da al’adu a duniya, tana kuma mai fatan samar da sabbin damammaki bisa ci gaban da take samu, da kuma hadin kai da kasashen Afirka ciki har da Benin, don tabbatar da ci gaban da aka samu, a dandalin tattaunawar hadin kan Sin da Afrika, da ingiza shawarar “ziri daya da hanya daya”, da shawarar raya duniya ta bai daya, da ma ajandar 2063 ta AU, da kuma tabbatar da tsare-tsaren bunkasuwar kasashen Afrika, har ma da goyon bayan kasashen nahiyar wajen samun farfadowar tattalin arziki, da bunkasuwa mai dorewa.

  • Ana Zura Ido Kan Yadda Amurka Za Ta Ki Raba-gari Da Kasar Sin

A nasa bangare, Patrice Talon cewa ya yi, shugabannin biyu sun kulla yarjejeniyar hadin gwiwarsu a fannoni daban-daban, ciki har da zurfafa hadin kai wajen tabbatar da shawarar “ziri daya da hanya daya”, da samun bunkasuwa, tare da kiyaye muhalli, da kayayyakin aikin gona, da kiwo lafiya da sauransu. Ban da wannan kuma, an gabatar da sanarwar kafa dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare tsakanin kasashen biyu.

Sannan, a Laraba ne shugaban kasar Sin Xi Jinping ya taya takwaransa na kasar Zimbabwe Emmerson Dambudzo Mnangagwa, murnar zarcewa a mukamin shugaban kasa.

A sakon na sa ta wayar tarho, shugaba Xi Jinping ya nuna cewa, Sin da Zimbabwe na da hulda mai kyau. Kaza lika a shekarun baya-bayan nan, kasashen biyu na karfafa fahimtar juna a siyasance, tare da samun sakamako mai armashi a fannin hadin kai, da goyon bayan juna kan muradunsu masu tushe, a karkashin jagorancin shugabannin biyu.

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

Xi ya kara da cewa, Sin na dora muhimmanci matuka kan bunkasuwar huldar kasashen biyu, yana kuma mai fatan kara hadin kai da Emmerson Dambudzo Mnangagwa, a fannin ingiza samun sabon ci gaba, ta fuskar huldar abokantaka bisa manyan tsare-tsare, da kiyaye adalci da daidaito na kasa da kasa, da muradun bai daya na kasashe masu tasowa.

Bugu da kari, a yau Juma’a shugaban kasar Sin Xi Jinping ya jajantawa takwaransa na kasar Afrika ta kudu Matamela Cyril Ramaphosa, bisa gobara da ta tashi a wani gini dake birnin Johannesburg, wadda kuma ta haddasa rasuwar mutane da dama.

Xi Jinping ya ce, a madadin gwamnatin Sin da jama’arta, yana jajantawa iyayen mamatan da bala’in ya ritsa da su. Ya ce, Sin na goyon bayan gwamnatin Afrika ta kudu da jama’arta. Ya kuma yi imanin cewa, a karkashin jagorancin Ramaphosa da gwamnatinsa, ba shakka jama’ar kasar za ta shawo kan wannan bala’in. (Amina Xu)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Madrid Za Ta Kasance Makonni Shida Ba Tare Da Vinicius Junior Ba

Next Post

Abinda Ya Kamata A Sani Game Da Jadawalin Gasar Kofin Zakarun Turai Na Bana 

Related

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

16 hours ago
Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?
Daga Birnin Sin

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

17 hours ago
Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe
Daga Birnin Sin

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

18 hours ago
An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

19 hours ago
Sin Ta Gabatar Da Korafi Da Babbar Murya Dangane Da Kalaman Jagoran Philippines 
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Korafi Da Babbar Murya Dangane Da Kalaman Jagoran Philippines 

20 hours ago
Xi Ya Bukaci A Yi Dukkan Mai Yiwuwa Wajen Gudanar Da Ayyukan Bincike Da Ceto Bayan Aukuwar Ambaliya A Lardin Gansu
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci A Yi Dukkan Mai Yiwuwa Wajen Gudanar Da Ayyukan Bincike Da Ceto Bayan Aukuwar Ambaliya A Lardin Gansu

21 hours ago
Next Post
Zakarun turai

Abinda Ya Kamata A Sani Game Da Jadawalin Gasar Kofin Zakarun Turai Na Bana 

LABARAI MASU NASABA

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

August 9, 2025
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

August 9, 2025
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

August 9, 2025
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

August 9, 2025
Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

August 9, 2025
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

August 9, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Jerin Ƴan Wasa Mata Da Suka Samu Kyautar Dala 100,000 Daga Gwamnatin Nijeriya

August 9, 2025
Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

August 9, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

August 9, 2025
ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.