• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Kaduna Ya Bude Masaukin Dalibai Mai Gado 400 Da Ofishin Hukumar Raya Birnin Zariya

by Sulaiman
2 years ago
Gwamnan Kaduna

Gwamnan jihar Kadauna, Sanata Uba Sani ya kaddamar da dakunan kwanan dalibai mai dauke da gadaje 400 a makarantar sakandiren mata ta gwamnati da ke Kawo da kuma katafaren ofishin hukumar raya birnin Zariya. 

 

Da yake jawabi a wajen kaddamar da ginin, Gwamna Uba ya bayyana ce wa, kammala aikin ginin kwanan daliban na daya daga cikin alkawuran da ya dauka na fifita ilimi a lokacin yakin neman zabe.

  • Gwamna Uba Sani Ya Kaddamar Da Fara Gina Makarantu 62.

A shekarar 2020 da ta gabata ne, dakunan daliban suka yi gobara, Gwamnan, ya nuna farin cikinsa da sake gina dakin kwanan daliban tare da gina karin ajujuwan karatu da nufin sake inganta ilimin yara mata.

 

LABARAI MASU NASABA

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

Da take jawabi, shugabar makarantar GGSS Kawo, Kaduna, Misis Victoria Hassan ta bayyana jin dadin ta kan kaddamar da dakunan da ajujuwan makarantar da Gwamna Uba Sani ya yi.

 

Hakazalika, Gwamna Uba Sani ya kuma kaddamar da katafaren ginin hukumar raya birnin Zariya.

 

A cewarsa, hukumar kula da birnin Zariya, za ta yi aiki ne kamar yadda takwarorinta na Kaduna da Kafanchan suke yi, an tsara su bisa irin tsarin takwararsu mai kula da birnin Abuja, domin su dinga kula da gari da gudanar da ayyuka, kamar gina tituna, kula da shara da kuma daidaita yanayin kasuwanci a yankin.

 

Ya nanata kudirin gwamnatinsa na ganin jihar Kaduna ta samu ci gaba cikin gaggawa, inda ya bayyana cewa, ba zai yi kasa a guiwa ba a kokarin da yake yi na sake inganta ababen more rayuwa da bunkasa tattalin arzikin jihar.

 

Tun da farko, shugabar hukumar raya birnin Zariya, Hajiya Balaraba ta bayyana cewa, tun bayan kafa hukumar, ta gudanar da ayyuka da dama kamar gina tituna da zamanantar da birnin tare da hadin guiwar hukumomin KADGIS, KASUPDA da sauran hukumomi.

Kazalika, hukumar ba a barta a baya ba wajen kwashe shara a birnin Zariya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Tsaro

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja
Tsaro

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Next Post
Matar Aure Ta Bukaci Kotu Ta Raba Aurenta Da Mijinta Saboda Yawan Jima’i

Kotu Za Ta Yanke Hukunci Kan Shari'ar Wani Limami A Abuja Da Sanata Ndume 6 Ga Satumba

LABARAI MASU NASABA

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025
Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.