ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Za Ta Yanke Hukunci Kan Shari’ar Wani Limami A Abuja Da Sanata Ndume 6 Ga Satumba

by Leadership Hausa
3 years ago
Kotu

Wata Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta dage shari’ar da ta ke sauraro har zuwa 6 ga watan Satumbar wannan shekara da muke ciki, wadda wani Limamin Masallacin Juma’a mai suna Imam Ibrahim Lawan ya shigar gabanta, inda yake zargin Sanata Ali Ndume da Mansur Jarkasa, a matsayin wadanda ke da hannu wajen tura guggun matasa ‘yan ta’adda su ci zarafinsa tare da yi masa mummunan rauni. Kazalika, ya zargi wadanda yake karar da cewa, sun hada ayarin ‘yan ta’addan ne da nufin hallaka shi, a masallacin da yake gabatar da Limanci na ‘Yan Majalisu a Apo da ke Zone B cikin Birnin Tarayya Abuja.

Kafin mai shari’a M. Muazu ya kai ga tsayar da ranar yanke hukuncin, ya baiwa Lauyan da ke kare wadanda ake zargin, wato Sanata da Mansir Jarkasa da kuma Jami’in ‘Yansanda  (CSP) Ibeh Chukwudi, damar kalubalantar karar da aka shigar a gaban Kotun.

  • Sin Ta Fara Shirin Aikewa Da Sinawa Zuwa Duniyar Wata Nan Zuwa 2030
  • Rage Radadin Cire Tallafi: Gwamnati Ta Baiwa  Kowacce Jiha Naira Biliyan Biyu A Kashin Farko

Kafin nan, an gabatar da shaidar da matar Limamin ta bayar mai suna Shamsiyya, inda ta bayyana cewa a ranar 16 ga watan Yunin 2023, Ndume ya yi sallah a wannan masallaci, ana kuma idarwa ne sai ya tashi ya fice daga masallacin a fusace, bisa zargin nasihar da Liman zai gabatar, ta shafe shi ne kai tsaye.

ADVERTISEMENT

Ta kara da cewa, “wanda a wannan lokaci, Liman ya yi kira kai tsaye ne tare da nusasshe da mutane a kan muhimmancin neman ilmi tare da aiki da shi, bisa koyarwar Alkur’ani da bin sunnar Annabi Muhammad SAW. Amma sai ga shi daga bisani Sanata ya dawo wannan masallaci yana kumfar baki da zage-zage tare da cin zarafinsa.”

Kamar yadda yake a rubuce a Kotu, wannan Uwargidan Liman ta hakikance cewa, ranar Lahadi wadda ta yi daidai da 18 ga watan Yunin wannan shekara, Maigidan nata (Liman) yana haramar tayar da Sallar La’asar a matsayinsa na Babban Limamin Masallacin, sai Ndume da Jarkasa tare da rakiyar guggun wasu mutane, suka fizge lasifikar da ke hannunsa suna kuma yi masa gargadi cewa, an dakatar da shi a matsayinsa na Babban Limamin wannan masallaci.

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

“Ganin faruwar hakan ya yi matukar ba shi mamaki da al’ajabi, inda ya dage sai ya aiwatar sallar abinsa kamar yadda ya saba, amma sai wani daga cikin dattawan masallacin ya ba shi shawara tare da jan hankalinsa nacewan ya yi hakuri ya fice daga masallacin don gudun tashin hankali, nan take ya dauki wannan shawara ya kuma fice daga masallacin,” in ji ta.

A cewar tata, ganin haka ne yasa Maigidan nata ya garzaya Ofishin ‘Yansanda na Apo, don shaida musu abin da ke faruwa domin gudun abin da ka je ya zo. Dawowar sa ke da wuya, “kafin ya ankara, gungun wasu matasa ‘yan ta’adda karkashin jagorancin Sanata Ndume da Jarkasa, suka far masa tare da dukan sa babu ji babu gani, wanda hakan ya yi sanadiyar samun mummunan rauni a kansa.”

Wannan dalili ne ya sa, Lauyan mai kara (Liman), Al-bashir Lawal Likko, ya nemi wannan Kotu da ta dubi irin wannan cin zarafi da keta haddi da zalinci da kuma mummunan raunin da aka yi wa wannan mai kara, wanda ko shakka bau ya saba wa doka da kuma kundirin tsarin mulkin wannan kasa, a yi masa adalci tare da kwato masa ‘yanci na wannan mummunan zalinci da aka yi masa.

Lauyan ya kara da cewa, lokacin da aka shigar da rahoto a Ofishin ‘Yansanda na Apo, wanda yake karewa (Liman) da wasu wadanda ke tare da shi, sai aka bi su duka aka kame wai da sunan masu kokarin tayar da tarzoma a tsakanin al’umma, aka kuma gurfanar da su a Kotun Magistiri da ke Abuja.

Sai kuma a bangaren wadanda ake karar, ma’ana Sanata Ndume da Jarkasa, Lauyansu Ben Jones Akpan, ya nemi Kotun ta yi watsi da kara a matsayin wani batu mara tushe da kan gado.

Har wa yau, ya bayyana wa Kotun cewa tuni kwamatin wannan masallaci ya dakatar Limamin, sakamakon zargin sa da ake yi da rashin gudanar da al’amuran masallacin yadda ya kamata da kuma barin wadanda ba su dace ba, marasa kuma alaka da masallacin su rika kwana a ciki, wanda hakan ya saba wa dokar masallacin.

Yanzu haka dai, Kotun ta dage shari’ar tare da tsayar da ranar 6 ga watan Satumbar wannan shekara a matsayin ranar yanke hukuncin. Inda mai karar ke ci gaba da ikrarin cewa, yana nan a kan bakarsa na kokarin neman hakkinsa, babu gudu babu ja da baya.

Kotu
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
Ra'ayi Riga

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Next Post
Zamfara: Shugabanninmu, Ku Yi Hankali Da ‘Yan Kanzagi

Zamfara: Shugabanninmu, Ku Yi Hankali Da ‘Yan Kanzagi

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.