ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Za Ta Yanke Hukunci Kan Shari’ar Wani Limami A Abuja Da Sanata Ndume 6 Ga Satumba

by Leadership Hausa
3 years ago
Kotu

Wata Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta dage shari’ar da ta ke sauraro har zuwa 6 ga watan Satumbar wannan shekara da muke ciki, wadda wani Limamin Masallacin Juma’a mai suna Imam Ibrahim Lawan ya shigar gabanta, inda yake zargin Sanata Ali Ndume da Mansur Jarkasa, a matsayin wadanda ke da hannu wajen tura guggun matasa ‘yan ta’adda su ci zarafinsa tare da yi masa mummunan rauni. Kazalika, ya zargi wadanda yake karar da cewa, sun hada ayarin ‘yan ta’addan ne da nufin hallaka shi, a masallacin da yake gabatar da Limanci na ‘Yan Majalisu a Apo da ke Zone B cikin Birnin Tarayya Abuja.

Kafin mai shari’a M. Muazu ya kai ga tsayar da ranar yanke hukuncin, ya baiwa Lauyan da ke kare wadanda ake zargin, wato Sanata da Mansir Jarkasa da kuma Jami’in ‘Yansanda  (CSP) Ibeh Chukwudi, damar kalubalantar karar da aka shigar a gaban Kotun.

  • Sin Ta Fara Shirin Aikewa Da Sinawa Zuwa Duniyar Wata Nan Zuwa 2030
  • Rage Radadin Cire Tallafi: Gwamnati Ta Baiwa  Kowacce Jiha Naira Biliyan Biyu A Kashin Farko

Kafin nan, an gabatar da shaidar da matar Limamin ta bayar mai suna Shamsiyya, inda ta bayyana cewa a ranar 16 ga watan Yunin 2023, Ndume ya yi sallah a wannan masallaci, ana kuma idarwa ne sai ya tashi ya fice daga masallacin a fusace, bisa zargin nasihar da Liman zai gabatar, ta shafe shi ne kai tsaye.

ADVERTISEMENT

Ta kara da cewa, “wanda a wannan lokaci, Liman ya yi kira kai tsaye ne tare da nusasshe da mutane a kan muhimmancin neman ilmi tare da aiki da shi, bisa koyarwar Alkur’ani da bin sunnar Annabi Muhammad SAW. Amma sai ga shi daga bisani Sanata ya dawo wannan masallaci yana kumfar baki da zage-zage tare da cin zarafinsa.”

Kamar yadda yake a rubuce a Kotu, wannan Uwargidan Liman ta hakikance cewa, ranar Lahadi wadda ta yi daidai da 18 ga watan Yunin wannan shekara, Maigidan nata (Liman) yana haramar tayar da Sallar La’asar a matsayinsa na Babban Limamin Masallacin, sai Ndume da Jarkasa tare da rakiyar guggun wasu mutane, suka fizge lasifikar da ke hannunsa suna kuma yi masa gargadi cewa, an dakatar da shi a matsayinsa na Babban Limamin wannan masallaci.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

“Ganin faruwar hakan ya yi matukar ba shi mamaki da al’ajabi, inda ya dage sai ya aiwatar sallar abinsa kamar yadda ya saba, amma sai wani daga cikin dattawan masallacin ya ba shi shawara tare da jan hankalinsa nacewan ya yi hakuri ya fice daga masallacin don gudun tashin hankali, nan take ya dauki wannan shawara ya kuma fice daga masallacin,” in ji ta.

A cewar tata, ganin haka ne yasa Maigidan nata ya garzaya Ofishin ‘Yansanda na Apo, don shaida musu abin da ke faruwa domin gudun abin da ka je ya zo. Dawowar sa ke da wuya, “kafin ya ankara, gungun wasu matasa ‘yan ta’adda karkashin jagorancin Sanata Ndume da Jarkasa, suka far masa tare da dukan sa babu ji babu gani, wanda hakan ya yi sanadiyar samun mummunan rauni a kansa.”

Wannan dalili ne ya sa, Lauyan mai kara (Liman), Al-bashir Lawal Likko, ya nemi wannan Kotu da ta dubi irin wannan cin zarafi da keta haddi da zalinci da kuma mummunan raunin da aka yi wa wannan mai kara, wanda ko shakka bau ya saba wa doka da kuma kundirin tsarin mulkin wannan kasa, a yi masa adalci tare da kwato masa ‘yanci na wannan mummunan zalinci da aka yi masa.

Lauyan ya kara da cewa, lokacin da aka shigar da rahoto a Ofishin ‘Yansanda na Apo, wanda yake karewa (Liman) da wasu wadanda ke tare da shi, sai aka bi su duka aka kame wai da sunan masu kokarin tayar da tarzoma a tsakanin al’umma, aka kuma gurfanar da su a Kotun Magistiri da ke Abuja.

Sai kuma a bangaren wadanda ake karar, ma’ana Sanata Ndume da Jarkasa, Lauyansu Ben Jones Akpan, ya nemi Kotun ta yi watsi da kara a matsayin wani batu mara tushe da kan gado.

Har wa yau, ya bayyana wa Kotun cewa tuni kwamatin wannan masallaci ya dakatar Limamin, sakamakon zargin sa da ake yi da rashin gudanar da al’amuran masallacin yadda ya kamata da kuma barin wadanda ba su dace ba, marasa kuma alaka da masallacin su rika kwana a ciki, wanda hakan ya saba wa dokar masallacin.

Yanzu haka dai, Kotun ta dage shari’ar tare da tsayar da ranar 6 ga watan Satumbar wannan shekara a matsayin ranar yanke hukuncin. Inda mai karar ke ci gaba da ikrarin cewa, yana nan a kan bakarsa na kokarin neman hakkinsa, babu gudu babu ja da baya.

Kotu
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?
  • Leadership Hausa
    An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

MASU ALAKA

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Kotu
Labarai

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Kotu
Labarai

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Next Post
Zamfara: Shugabanninmu, Ku Yi Hankali Da ‘Yan Kanzagi

Zamfara: Shugabanninmu, Ku Yi Hankali Da ‘Yan Kanzagi

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Kotu

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Kotu

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.