• English
  • Business News
Friday, May 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Umarci Jakadun Nijeriya Da Su Dawo Gida

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Tsadar Rayuwa: Tinubu Na Duba Yiwuwar Dawo Da Tallafin Mai Na Wucin Gadi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya umarci dukkanin jakadun Nijeriya da su dawo gida.

Ministan kula da harkokin wajen Nijeriya, Ambasada Yusuf Tuggar, shi ne ya shaida hakan a ranar Asabar.

  • ‘Yan Nijeriya Na Dandana Kudarsu A Mulkin Tinubu — PDP

A wata sanarwar babban hadimin ministan kan yada labarai da hulda da jama’a, Alkasim Abdulkadir, ya tabbatar da cewa dukkanin Jakadun Nijeriya an kirayesu da su dawo.

Sanarwar ta ce, “Bisa tambayar da ake ta yi dangane da wasikar kiranye ga jakadan Nijeriya a Ingila, ministan harkokin wajen Nijeriya, Ambasada Yusuf Maitama Tuggar, ya warware zare da abawa da cewa dukkanin Jakadun Nijeriya ne ma aka umarta da su dawo gida bisa umarnin da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bada.

“Dukkanin Jakadun Nijeriya da suke wakilci a wasu kasashe suna karkashin umarnin shugaban kasa ne, kuma shi ne ke da ikon dawo da dukkanin wani daga kowace kasa.”

Labarai Masu Nasaba

Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa

‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano

A cewarsa, fayyace hakikanin batun ya zama musu dole ne lura da kiran da aka yi wa Jakadan Nijeriya a kasar Burtaniya, Sarafa Ishola da ya dawo.

A wasika mai dauke da kwanan wata 31 ga watan Agustan 2023 da ministan harkokin wajen ya aika wa Ishola, Tuggar na cewa, “Ina farin cikin sanar da kai matakin da shugaban kasa ya dauka na maka kiranye, hakan da ke nuni da zuwan karshen wakilcinka a matsayin babban jakadan Nijeriya a kasar Ingila.”

Kan wannan, an umarci jakadan da cewa cikin kwanaki shida ya hada bayanan barin aiki sannan ana tsammanin zai dawo Nijeriya kafin ko zuwa ranar 31 ga watan Oktoba, 2023.

“Ina amfani da wannan damar wajen nuna godiyar shugaban kasa a gareka bisa gudunmawarka da ka bayar a matsayin babban jadakan Nijeriya a Burtaniya.

“A daidai lokacin da muke tsumayar dawowarka Abuja, shugaban kasa na mika godiyarsa gareka bisa hidimta wa Nijeriya na zama babban jakadanta. Ina maka fatan samun rayuwa mai kyau a nan gaba,” wasikar ta shaida.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sana’a Ce Rufin Asirin Mace —Hindatu

Next Post

Gwamnatin Tarayya Ta Shirya Don Fara Rigakafin Kansar Mahaifa

Related

Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa
Manyan Labarai

Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa

40 minutes ago
Yadda Rikici Ya Yi Sanadin Kashe DPO A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano

13 hours ago
Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja
Labarai

Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

14 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa

15 hours ago
Atiku Ya Caccaki Gwamnatin Tinubu, Ya Yi Gargaɗi Kan Cin Sabon Bashi
Manyan Labarai

Atiku Ya Caccaki Gwamnatin Tinubu, Ya Yi Gargaɗi Kan Cin Sabon Bashi

19 hours ago
Zaman lafiya
Labarai

MDD Ta Gudanar Da Bikin Ranar Tunawa Da Dakarun Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Duniya Ta 2025

21 hours ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Shirya Don Fara Rigakafin Kansar Mahaifa

Gwamnatin Tarayya Ta Shirya Don Fara Rigakafin Kansar Mahaifa

LABARAI MASU NASABA

Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa

Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa

May 30, 2025
Cutar Hawan Jini Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke

Cutar Hawan Jini Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke

May 30, 2025
Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo

Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo

May 29, 2025
An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 

An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 

May 29, 2025
Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600

Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600

May 29, 2025
Yadda Rikici Ya Yi Sanadin Kashe DPO A Kano

‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano

May 29, 2025
Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda

Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda

May 29, 2025
Sin Ta Cimma Nasasar Harbar Na’urar Nazarin Tauraro a Sararin Sama Mai Lakabin “Tianwen-2”

Sin Ta Cimma Nasasar Harbar Na’urar Nazarin Tauraro a Sararin Sama Mai Lakabin “Tianwen-2”

May 29, 2025
Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

May 29, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa

May 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.