ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

by Sulaiman
10 months ago
Soludo

Gwamnan jihar Anambra, Farfesa Chukwuma Charles Soludo, ya bayyana cewa ba shi da wata nadama kan goyon bayan da ya nuna a fili ga Shugaban Ƙasa, Bola Tinubu, duk da kasancewarsa a jam’iyyar adawa.

 

Soludo ya bayyana haka a ranar Talata yayin da yake zantawa da manema labarai a fadar shugaban ƙasa bayan wata ganawa da Tinubu a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 
  • ’Yan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 6 A Taraba

Ya bayyana ganawar a matsayin mai ciki da daɗi, ya kuma ya yaba da yanayin lafiyar Shugaba Tinubu. “Shugaban Ƙasa yana cikin ƙoshin lafiya da kuzari, kuma na ji daɗin ganawa da shi. Lallai ganawa ce mai matuƙar daɗi da farinciki,” in ji Soludo.

 

LABARAI MASU NASABA

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Da aka tambaye shi dalilin da ya sa ya fito ƙarara ya goyi bayan shugaban ƙasa wanda ba a cikin jam’iyyarsu yake, Soludo ya ce goyon bayansa ga Tinubu ba sabon abu ba ne.

 

“An samar da waɗannan huluna tun lokacin da Shugaban Ƙasa ya ziyarci Jihar Anambra kuma kun ga allunan talla da sauran abubuwa da ke bayyana cewa masu ra’ayin kowa ci gaba suna aiki tare ne da juna,” in ji Soludo.

 

“Bayan haka, wannan wata babbar manufa ce da na yi imani da ita sosai, cewa ya kamata dukkan jam’iyyun siyasa da ke ikirarin ra’ayin ci gaba su haɗu a ƙarƙashin wata babbar ƙawance don zurfafa tunani da kawo ci gaba ba kawai a tafarkin dimokuradiyyarmu ba, har ma da ci gaban tattalin arziki da zamantakewar kasarmu.”

 

Gwamnan ya jaddada cewa kiransa na ganin masu ra’ayin ci gaba sun yi aiki tare ya samo asali ne daga yaƙini da kuma daɗaɗɗiyar alaƙar da ke tsakaninsa da Shugaban Ƙasa.

 

“Idan na ce masu ra’ayin ci gaba su yi aiki tare, kira ne ga duk masu magana kan Shugaba Bola Ahmed Tinubu… Ina nufin, ba ni da wani uzuri game da hakan.

 

“Shugaba Tinubu abokina ne, abokina ne tun shekaru 22 da suka gabata zuwa yanzu.

 

“Abokina ne, ina goyon bayansa, kuma na gamsu da matakan da ya ɗauka, musamman a fannin tattalin arziki, kuma na bayyana hakan ba sau ɗaya ba, muna kan hanyar ƙwarai kuma muna buƙatar mu ci gaba a haka,” in ji Soludo.

 

Game da halin tsaro a Jihar Anambra, gwamnan ya ce gwamnatinsa ta ɗauki wani tsari na bai-daya tun daga watan Janairu, biyo bayan zartar da dokar tsaron cikin gida a jihar.

 

“Ana kokarin tunkarar matsalar rashin tsaro ne tun daga tushe. Dukkanin miyagun ‘yan ta’adda sun tsere daga jihar saboda su ne ke yaudarar matasanmu da kuma jefa su cikin aikata laifuka,” in ji shi.

 

Soludo ya ce gwamnati na amfani da matakan karfi da na lallashi don magance matsalar rashin tsaro.

Soludo
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware
  • Sulaiman
    Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma
  • Sulaiman
    Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin
  • Sulaiman
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

MASU ALAKA

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa
Manyan Labarai

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Rahotonni

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

June 19, 2026
Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
Labarai

Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

June 19, 2026
Next Post
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam'iyar ADC Ta Yi

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Abinci

Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

June 19, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

June 19, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

June 19, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

June 19, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

June 19, 2026
Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

June 19, 2026
Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.