• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Bullar Cutar Gansakuka Ta Sa Manoman Citta Tafka Mummunar Asara A Kaduna

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Kalubalen Da Manoman Shinkafa Ke Fuskanta A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Kaduna, na fuskantar barazanar tafka asarar naira biliyan 10, sakamakon bullar cutar Gansakuka da ke yi wa Citta illa, wanda hakan ya sa wasu daga cikin Manoman cittar fadin a jihar, suka bukaci a kawo musu daukin gaggawa.

Sakamakon bullar  cutar  a Kudancin Kaduna,  Kungiyar Manoma Cittar ta Kasa (NGAN), tare da hadin guiwar wasu wadanda ba Manoma ba, sun tallafa wa Manoman Citta 18; kowannensu da naira 50,000, domin rage musu radadin annobar cutar.

  • Hajjin Badi: Dalilin Kara Kudin Kujera Zuwa Naira Miliyan 4.5 – NAHCON
  • Share Fagen Gasar Kofin Duniya; Messi Ya Zura Kwallo A Ragar Ecuador

Kazalika, kungiyar Manoman Cittar ta bayyana cewa, kakar noman Citta ta shekarar 2023 a Kudancin Kaduna, ta samu babbar koma baya, sakamakon bullar wannan cuta, inda ta koka kwarai da gaske a kan cewa, hakan ya yi matukar jawo asarar sama da naira biliyan 10, da ya kamata a shigar a wani fannin da ya shafi tattalin arzkin jihar.

A taron manema labarai na Karamar Hukumar  Kachia da ke Jihar ta Kaduna, Shugbana Kungiyar na kasa N.B Daudu, ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da kuma ta Jihar Kaduna, da su samar da sinadaran karya cutar ta Gansakuka.

Bugu da kari, da yake yin tsokaci a kan noman Cittar, Shugaban ya sanar da cewa, sakamakon rashin samun inda ake sarrafa Cittar, yasa ba ta iya shiga gasa a kasuwar duniya.

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

Daudu ya sanar da cewa, akwai bukatar a samar da inda za a rika sarrafa ta, domin kai wa wani mataki a duniya.

Ya kara da cewa, rashin sarrafa ta da kuma yadda ake hada ta, ya janyo ana barin Nijeriya a baya wajen nomanta da kuma fitar da ita zuwa kasashen ketare .

Su ma a nasu jawaban, Shugaban Karamar Hukumar Kachia Aaron Bako da kuma Daraktar Ma’aikatar aikin noma da kula da gandun daji, Kueen Saidu sun sanar da cewa, noman Citta shi ne sana’ar da al’ummar yankin suka fi mayar da hankali a kai, domin samar wa kansu da kudaden shiga.

A cewar tasu, fannin noman Citta a yankin na bayar da gagarumar gudunmawa wajen kara habaka tattalin arzikin wannan kasa, shi yasa muke kira ga matakan gwamantin kasar nan, da su taimaka wa Manoman Cittar a yankunan da wannan cuta ta yi wa gonakansu illa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sabuwar Hanyar Kwacen Shafin Facebook (I)

Next Post

Wata Girgizar Kasa Mai Karfi Ta Kashe Fiye Da Mutum 820 A Morocco

Related

Neja
Noma Da Kiwo

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

2 hours ago
Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

1 week ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

2 weeks ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

2 weeks ago
Next Post
Wata Girgizar Kasa Mai Karfi Ta Kashe Fiye Da Mutum 820 A Morocco

Wata Girgizar Kasa Mai Karfi Ta Kashe Fiye Da Mutum 820 A Morocco

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.