ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kai Karar Gwamnatin Japan Gaban Kotu Da Al’ummar Kasar Suka Yi Saboda Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukilya A Cikin Teku Mafari Ne Kawai

by CMG Hausa
2 years ago
Japan

Jiya Jumma’a 8 ga watan Satumba, al’ummar kasar Japan sama da dari sun gabatar da kara ga wata kotun dake yankin Fukushima na kasar Japan, inda suka zargi gwamnatin kasar gami da kamfanin samar da wutar lantarki na Tokyo wato Tokyo Electric Power Company a turance, da aikata laifin zubar da ruwan dagwalon nukiliya a cikin teku ba bisa doka ba, tare da bukatar kotun da ta yanke musu hukuncin dakatar da wannan danyen aiki, abun da ya kasance kara ta farko da aka gabatar dangane da bukatar dakatar da zubar da ruwan dagwalon nukiliya cikin teku a kasar Japan, kana, kokari ne na daban da jama’ar kasar suka yi na kare hakkokinsu bisa doka, bayan da wasu kungiyoyin al’umma suka gabatar da kara kan firaministan kasar, Fumio Kishida.

Takardar kai karar ta ce, kafin ta fara zubar da ruwan dagwalon nukiliya a cikin teku, gwamnatin Japan ba ta taba gudanar da bincike a fannonin gurbata muhalli ko illoli ga muhallin halittu ba, kana, kamfanin samar da wutar lantarki na Tokyo na iya kara kafa manyan tankunan ajiye ruwan dagwalon nukiliyar maimakon zubarwa a cikin teku.

Don haka, al’ummar Japan na ganin cewa, gwamnatin kasar gami da kamfanin samar da wutar lantarki na Tokyo sun aikata laifin gurbata muhalli, da keta hakkokinsu a fannin kamun kifi da tafiyar da rayuwa cikin kwanciyar hankali, abu ne da ya keta doka.

ADVERTISEMENT

Zubar da ruwan dagwalon nukiliya a cikin teku da gwamnatin kasar Japan take yi, babbar kasada ce da ba a taba ganin irinta ba a tarihi, wanda ke da alakar kut da kut da tsabtar muhallin yankunan teku a duniya, da lafiyar dan Adam gami da muradun zuriyoyinmu dake tafe.

Kai karar gwamnati da al’ummar Japan suka yi, ya shaida babbar damuwa daga bangarori daban-daban gami da Allah wadai da suka yi. Kwararru na ganin cewa, abun da wadannan mutanen Japan suka yi, zai iya kara karfafa gwiwar sauran mutane don su kiyaye hakkokinsu bisa doka ta hanyoyi daban-daban. (Murtala Zhang)

LABARAI MASU NASABA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara
Daga Birnin Sin

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka
Daga Birnin Sin

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Next Post
Rashin Tausayi ‘Ina Fama Da Talauci, ‘Yan’uwana Masu Hali Sun Ki Taimako Na’

Rashin Tausayi ‘Ina Fama Da Talauci, ‘Yan’uwana Masu Hali Sun Ki Taimako Na’

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Ceton Dukkan Ɗalibai 230 Da Aka Sace A Neja

Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Ceton Dukkan Ɗalibai 230 Da Aka Sace A Neja

December 22, 2025
Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

December 22, 2025
An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.