• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Idris Ya Nada Dan Marigayi Sheikh Giro Mukami A Hukumar Alhazai Ta Kebbi

by Muhammad
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Gwamna Idris Ya Nada Dan Marigayi Sheikh Giro Mukami A Hukumar Alhazai Ta Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Nasir Idris na Jihar Kebbi ya nada, Hussaini Abubakar-Giro, a matsayin mamba a hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kebbi, don maye gurbin mahaifinsa, Sheik Abubakar Giro, wanda ya rasu a ranar Laraba.

Kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’a Wa’iqamatus Sunnah ta kasa (JIBWIS) ta kasa ta roki Gwamnan da ya duba daya daga cikin ‘ya’yan marigayin kan mukamin da aka bai wa mahaifinsu wanda Gwamnan ya amince da hakan.

  • Tinubu Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Babban Malamin Addinin Musulunci Giro Argungu
  • NUJ Kebbi Ta Yi Alhini Rasuwar Tsohon dan Jarida Ibrahim Argungu

Alhaji Ahmed Idris, Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamnan ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Birnin Kebbi ranar Lahadi.

Ahmed Idris ya bayyana cewa gwamnan ya amince da nadin ne a lokacin da ya karbi bakuncin shugabannin kungiyar (JIBWIS) karkashin jagorancin shugaban kungiyar na kasa, Sheik Abdullahi Bala-Lau, wanda ya kai ziyarar ta’aziyya ga gwamnan a gidan gwamnati da ke Birnin Kebbi.

Gwamnan ya tabbatar wa kungiyar Izalar cewa an riga an karbi wannan kiran.

Labarai Masu Nasaba

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Idris ya godewa kungiyar bisa wannan ziyarar, inda ya ce: “Rashin ba ga iyalansa kadai ya shafa ba har kowa da kowa.”

Ya ce Abubakar Giro wani ginshiki ne na yada addinin Musulunci a kasashen Afirka da dama, ya kuma yi addu’ar Allah Ta’ala ya gafarta masa kurakuransa, ya karbi ayyukansa na alheri, ya saka masa da Jannatul Firdaus.

Malaman sun kuma gabatar da addu’o’i na musamman ga marigayin, da sauran musulmin da suka rasu tare da addu’ar samun zaman lafiya a dukkan sassan Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Giro ArgunguGwamna KebbiNasir AhmadSheikh Giro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Brazil Ta Cire Sunan Antony Daga Tawagarta Saboda Zargin Dukan Budurwarsa

Next Post

Gwamnonin Arewa Maso Gabas Sun Koka Kan Kwararar ‘Yan Bindiga Zuwa Jihohinsu

Related

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

13 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

22 hours ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

24 hours ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

1 day ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

2 days ago
Next Post
Gwamnonin Arewa Maso Gabas Sun Koka Kan Kwararar ‘Yan Bindiga Zuwa Jihohinsu

Gwamnonin Arewa Maso Gabas Sun Koka Kan Kwararar ‘Yan Bindiga Zuwa Jihohinsu

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.