• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karar Zaben Shugaban Kasa: Ko Ya Za Ta Kaya A Kotun Koli?

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Zaben Shugaban Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan da kotun sauraron karar shugaban kasa ta yi fatali da kararrakin da ‘yan takarar jam’iyyun adawa suka shigar a gabanta na kalubalantar nasarar Bola Ah-med Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa da ya gudana a ran-ar 25 ga Fabrairu, yanzu haka ‘yan Nijeriya sun zuba ido su ga yadda za ta kaya a kotun koli.

Bai zo wa ‘yan Nijeriya da mamaki ba, lokacin da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar da takwaransa na jam’iyyar LP, Mista Peter Obi suka ki amincewa da hukuncin kotun sauraron karar shugaban kasa da ta zantar na tabbatar da nasarar Tinubu a zaben 2023.

  • Kotun Zaben Gwamnan Taraba: Cikin Matsi INEC Ta Ayyana Sakamako, A Sake Bitar Zaben – NNPP

A lokacin da yake zantawa da ‘yan jarida dangane da hukuncin kotun a sakateri-yar jam’iyyar PDP a Abuja, Atiku ya bayyana cewa kasancewarsa dan gwag-warmayar siyasa a cikin rayuwasa zai ci gaba da fafatuka ba zai taba ja da baya ba.

A nasa bangaren da yake zantawa da manema labarai a Onitsha da ke Jihar Anambra, Obi ya ce ya bukaci lauyoyinsa su gaggauta kalubalen da ke cikin hukuncin kotun da alkalai biyar suka zantar karkashin shugabancin mai shari’a Simon Haruna Tsamani.

Yayin da Atiku ya ce yana mutunta hukuncin kotu, amma dai ya yi watsi da wan-nan hukunci. Ya lura cewa an gudanar da zaben bisa hanyar da bai kamata ba, wanda akwai bukatar bangaren shari’a ta samar da mafita.

Labarai Masu Nasaba

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

Ya kara da cewa ya umurci lauyoyinsa su yi amfani da damar da tsarin mulki ya bayar domin ci gaba da kalubalantar shari’ar a kotun koli.

Haka shi Obi ya ce duk da yana girmama hukuncin kotu, amma bai amince da da-lilan da kotun ta bayar ba wajen zantar da hukunci.

“Dama ta ce a matsayina na dan takarar shugaban kasa da kuma manufar jam’iyyar LP in kalubalanci wannan hukunci ta hanyar daukaka kara cikin gagga-wa kamar yadda kundin tsarin mulkin Nijeriya ya tanada,” in ji shi.

Idan za a iya tunawa lokacin da kotun sauraron karar zaben shugaban kasa ta zantar da hukunci a wani zama da ta yi na tsawon awa 12 a ranar Laraba da ta gabata, kotun karkashin jagorancin Tsammani ta tabbatar da nasarar Shugaba Tinubu a matsayin halartaccen shugaban kasa.

Ta ce kararrakin da jam’iyyu guda uku suka shigar bisa kalubalantar nasarar Tinubu, “Dukkanin kararrakin ba su da nagarta. Domin haka ta yi watsi da kararrakin.

“Wadannan kararraki ba su da nagarta. Na tabbatar da nasarar Bola Ahmed Tinubu a matsayin zababben shugaban kasan Nijeriya. Jam’iyyun sun gaza gamsar da kotun da kwararan hujjoji, domin haka wannan kotun ta zantar da hukuncinta na karshe.

Fusatattun jam’iyyun da ‘yan takaransu sun jaddada cewa ba a gudanar da zaben bisa ka’idojin da dokokin zabe da kundin tsarin mulki na shekarar 1999 suka shimfida ba.

Cikin kararrakin da aka gabatar a gaban kotu kan kalubalantar Tinubu sun hada da rashin samun kashi 25 na kuri’u a Babban Birnin Tarayya (Abuja). Haka kuma akwai rashin saka sakamaon zaben a na’ura da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ba ta yi ba, wanda hakan suke ganin ya sa Tinubu ya samu nasara a zaben.

Haka kuma masu shigar da kara sun yi zargin an tafka magudi a zaben, wanda aka samu kuri’u fiye da kima da kuma bayar da cin hanci da rashawa a lokacin gudanar da zaben.

A cikin kararrakin, jam’iyyar APM ta bukaci kotun ta soke zaben shugaban kasa bisa dalilin zaben Sanata Kashim Shettima a matsayin mataimakin shugaban kasa, wanda take ganin cewa bai kamata Shettima ya zama mataimakin shugaban kasa a jam’iyyar APC ba, saboda yana rake da mukamin dan majalisar dattawa na Jihar Borno.

Kotun ta fara watsi ne da karar da jam’iyyar APM ta shigar na zaber Shettima a matsayin mataimaki. Jagoran kotun, mai shari’a Tsammani ya yi watsi da karar ne bisa rashin nagarta. Sannan ya ce INEC tana da hurumin kin saka sakamakon zaben a na’ura.

Bisa batun korafin rashin samun kashi 25 da Tinubu bai yi ba a Abuja kuwa, kotun ta ce Abuja daidai take da kowacce jiha, babu wata jiha da ta fi wata. Ta kuma yi watsi da batun karar da Atiku ya shigar na cewa Tinubu yana amfani da takardar shaidan dan kasa guda biyu.

Yayin da Shugaba Tinubu da magoya bayan jam’iyyarsa ke murna da hukuncin kotun, lamarin ya kasance mara dadi ga magoya bayan PDP da LP.

Duk da dai kundin tsarin mulki ya bai wa Atiku da Obi hurumin zuwa kotun koli, mutane da dama na ganin cewa bata lokaci ne su ci gaba da kalubalantar hukuncin kotun.

Dangane da abubuwan da suka wakana a kotun sauraron karar zaben shugaban kasa, manazarta da daman a ganin cewa wace sabuwar shaida za su iya gabatarwa a kotun koli har su iya samun nasara.

Da yake tabbatar da dalilin da ya sa aka yi watsi da korar Obi, wani mai sharhi kan al’amuran yau da kullum, Philip Okon ya ce, “Na ce karar da Obi ya shigar ba ta da nagarta. Idan ka yi ikirarin cewa ka samu kuri’u masu rinjaye, ya kamata ka bayyana adadin kuri’un da ka samu wanda ya sa ka yi nasara, sannan ka bayyana adadin kuri’un da abokan hamayyarka suka samu wanda ya sa suka yi rashin na-sara. Yana da sauki kamar A,B, C, D. Abin da Hope Uzodimma ya yi kenan a rikicin zaben gwamna.

“Ba za ku iya yin ikirarin cewa kun sami rinjayen kuri’u ba tare da gaya wa kotu adadin kuri’un da kuka samu da kuma rumfunan zabe da kuka samu kuri’u ba. Ba abu ne mai sauki a iya tabbatar da cewa kun ci zabe ba, domin abin da kotun sau-raren karar take nema kenanan, wanda rashin gamsar da ita har ya sa ta yi watsi da karar.”

Okon ya kara cewa idan aka ci gaba da tafiya a haka, ya kamata ‘yan Nijeriya su tashi tsaye don ganin an yi wa kundin tsarin mulkin kwaskwarima wajen tabbatar an kammala shari’ar zabe kafin a rantsar da wadanda suka yi nasara.

A daidai lokacin da shari’ar ta dangana da kotun koli, ‘yan Nijeriya sun zuba ido domin ganin yadda masu shigar da kara za su iya gabatar da sabbin hujjoji da za su iya gamsar da kotu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KotuShugaban KasaZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Sanya Wasu Kamfanonin Tsaron Amurka Biyu Takunkumi

Next Post

Hukumar Kididdigar Sin Ta Gabatar Da Manyan Alkaluman Tattalin Arziki Na Watan Agusta

Related

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

3 days ago
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

1 week ago
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa
Tambarin Dimokuradiyya

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

1 week ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

1 month ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

1 month ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

1 month ago
Next Post
Sin

Hukumar Kididdigar Sin Ta Gabatar Da Manyan Alkaluman Tattalin Arziki Na Watan Agusta

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.