ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karar Zaben Shugaban Kasa: Ko Ya Za Ta Kaya A Kotun Koli?

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Zaben Shugaban Kasa

Bayan da kotun sauraron karar shugaban kasa ta yi fatali da kararrakin da ‘yan takarar jam’iyyun adawa suka shigar a gabanta na kalubalantar nasarar Bola Ah-med Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa da ya gudana a ran-ar 25 ga Fabrairu, yanzu haka ‘yan Nijeriya sun zuba ido su ga yadda za ta kaya a kotun koli.

Bai zo wa ‘yan Nijeriya da mamaki ba, lokacin da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar da takwaransa na jam’iyyar LP, Mista Peter Obi suka ki amincewa da hukuncin kotun sauraron karar shugaban kasa da ta zantar na tabbatar da nasarar Tinubu a zaben 2023.

  • Kotun Zaben Gwamnan Taraba: Cikin Matsi INEC Ta Ayyana Sakamako, A Sake Bitar Zaben – NNPP

A lokacin da yake zantawa da ‘yan jarida dangane da hukuncin kotun a sakateri-yar jam’iyyar PDP a Abuja, Atiku ya bayyana cewa kasancewarsa dan gwag-warmayar siyasa a cikin rayuwasa zai ci gaba da fafatuka ba zai taba ja da baya ba.

ADVERTISEMENT

A nasa bangaren da yake zantawa da manema labarai a Onitsha da ke Jihar Anambra, Obi ya ce ya bukaci lauyoyinsa su gaggauta kalubalen da ke cikin hukuncin kotun da alkalai biyar suka zantar karkashin shugabancin mai shari’a Simon Haruna Tsamani.

Yayin da Atiku ya ce yana mutunta hukuncin kotu, amma dai ya yi watsi da wan-nan hukunci. Ya lura cewa an gudanar da zaben bisa hanyar da bai kamata ba, wanda akwai bukatar bangaren shari’a ta samar da mafita.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Ya kara da cewa ya umurci lauyoyinsa su yi amfani da damar da tsarin mulki ya bayar domin ci gaba da kalubalantar shari’ar a kotun koli.

Haka shi Obi ya ce duk da yana girmama hukuncin kotu, amma bai amince da da-lilan da kotun ta bayar ba wajen zantar da hukunci.

“Dama ta ce a matsayina na dan takarar shugaban kasa da kuma manufar jam’iyyar LP in kalubalanci wannan hukunci ta hanyar daukaka kara cikin gagga-wa kamar yadda kundin tsarin mulkin Nijeriya ya tanada,” in ji shi.

Idan za a iya tunawa lokacin da kotun sauraron karar zaben shugaban kasa ta zantar da hukunci a wani zama da ta yi na tsawon awa 12 a ranar Laraba da ta gabata, kotun karkashin jagorancin Tsammani ta tabbatar da nasarar Shugaba Tinubu a matsayin halartaccen shugaban kasa.

Ta ce kararrakin da jam’iyyu guda uku suka shigar bisa kalubalantar nasarar Tinubu, “Dukkanin kararrakin ba su da nagarta. Domin haka ta yi watsi da kararrakin.

“Wadannan kararraki ba su da nagarta. Na tabbatar da nasarar Bola Ahmed Tinubu a matsayin zababben shugaban kasan Nijeriya. Jam’iyyun sun gaza gamsar da kotun da kwararan hujjoji, domin haka wannan kotun ta zantar da hukuncinta na karshe.

Fusatattun jam’iyyun da ‘yan takaransu sun jaddada cewa ba a gudanar da zaben bisa ka’idojin da dokokin zabe da kundin tsarin mulki na shekarar 1999 suka shimfida ba.

Cikin kararrakin da aka gabatar a gaban kotu kan kalubalantar Tinubu sun hada da rashin samun kashi 25 na kuri’u a Babban Birnin Tarayya (Abuja). Haka kuma akwai rashin saka sakamaon zaben a na’ura da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ba ta yi ba, wanda hakan suke ganin ya sa Tinubu ya samu nasara a zaben.

Haka kuma masu shigar da kara sun yi zargin an tafka magudi a zaben, wanda aka samu kuri’u fiye da kima da kuma bayar da cin hanci da rashawa a lokacin gudanar da zaben.

A cikin kararrakin, jam’iyyar APM ta bukaci kotun ta soke zaben shugaban kasa bisa dalilin zaben Sanata Kashim Shettima a matsayin mataimakin shugaban kasa, wanda take ganin cewa bai kamata Shettima ya zama mataimakin shugaban kasa a jam’iyyar APC ba, saboda yana rake da mukamin dan majalisar dattawa na Jihar Borno.

Kotun ta fara watsi ne da karar da jam’iyyar APM ta shigar na zaber Shettima a matsayin mataimaki. Jagoran kotun, mai shari’a Tsammani ya yi watsi da karar ne bisa rashin nagarta. Sannan ya ce INEC tana da hurumin kin saka sakamakon zaben a na’ura.

Bisa batun korafin rashin samun kashi 25 da Tinubu bai yi ba a Abuja kuwa, kotun ta ce Abuja daidai take da kowacce jiha, babu wata jiha da ta fi wata. Ta kuma yi watsi da batun karar da Atiku ya shigar na cewa Tinubu yana amfani da takardar shaidan dan kasa guda biyu.

Yayin da Shugaba Tinubu da magoya bayan jam’iyyarsa ke murna da hukuncin kotun, lamarin ya kasance mara dadi ga magoya bayan PDP da LP.

Duk da dai kundin tsarin mulki ya bai wa Atiku da Obi hurumin zuwa kotun koli, mutane da dama na ganin cewa bata lokaci ne su ci gaba da kalubalantar hukuncin kotun.

Dangane da abubuwan da suka wakana a kotun sauraron karar zaben shugaban kasa, manazarta da daman a ganin cewa wace sabuwar shaida za su iya gabatarwa a kotun koli har su iya samun nasara.

Da yake tabbatar da dalilin da ya sa aka yi watsi da korar Obi, wani mai sharhi kan al’amuran yau da kullum, Philip Okon ya ce, “Na ce karar da Obi ya shigar ba ta da nagarta. Idan ka yi ikirarin cewa ka samu kuri’u masu rinjaye, ya kamata ka bayyana adadin kuri’un da ka samu wanda ya sa ka yi nasara, sannan ka bayyana adadin kuri’un da abokan hamayyarka suka samu wanda ya sa suka yi rashin na-sara. Yana da sauki kamar A,B, C, D. Abin da Hope Uzodimma ya yi kenan a rikicin zaben gwamna.

“Ba za ku iya yin ikirarin cewa kun sami rinjayen kuri’u ba tare da gaya wa kotu adadin kuri’un da kuka samu da kuma rumfunan zabe da kuka samu kuri’u ba. Ba abu ne mai sauki a iya tabbatar da cewa kun ci zabe ba, domin abin da kotun sau-raren karar take nema kenanan, wanda rashin gamsar da ita har ya sa ta yi watsi da karar.”

Okon ya kara cewa idan aka ci gaba da tafiya a haka, ya kamata ‘yan Nijeriya su tashi tsaye don ganin an yi wa kundin tsarin mulkin kwaskwarima wajen tabbatar an kammala shari’ar zabe kafin a rantsar da wadanda suka yi nasara.

A daidai lokacin da shari’ar ta dangana da kotun koli, ‘yan Nijeriya sun zuba ido domin ganin yadda masu shigar da kara za su iya gabatar da sabbin hujjoji da za su iya gamsar da kotu.

Zaben shugaban kasa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Zaben shugaban kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Sin

Hukumar Kididdigar Sin Ta Gabatar Da Manyan Alkaluman Tattalin Arziki Na Watan Agusta

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.