• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kano Ta Rungumi Ilimin Kimiyya Don Kyautata Rayuwar Jama’a – Kwamishina

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Kano

Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana aniyarta ta rungumar harkokin kimiyya da fahasa, domin kyautata rayuwar dumbin al’ummar da ke fadin jihar ta hanyar bayar da muhimmanci ga harkokin kimiyya da fasaha a jihar.

Kwamishinan Ma’aikatar Kimiyya, fasaha da kere-keren zamani na jihar, Muhammed Tajo Othman, wanda ya jagoranci babban sakatare da daraktocin ma’aikatar zuwa zagayen duba Cibiyar Musulunci ta Kura da Wudil da suke jihar, domin duba injinan wasan kwallon kafa da wasu injinan da aka yi watsi da su.

  • Ganduje Ya Magantu Kan Nasarar Jam’iyyar APC A Kano, Ya Ce Gawuna Zai Zo Wa Kano Da Alheri

Tajo Othman ya ce, Gwamnatin Alhaji Abba Kabir Yusuf, ta sanya hankali sosai wajen ganin ta yi amfani da harkokin kimiyya da fasaha da kere-kere, domin tabbatar da cewa a halin da ake ciki yanzu na kimiyya da fasaha na taimakawa sosai wajen bukatar ci gaba, don haka jihar ba za ta yi wasa da wannan fanni ko kadan ba.

Kwamishinan ya kara dacewa, ziyarar na kunshe ne da manufar duba halin da injinan suke ciki, domin ganin an bi matakan da suka dace wajen gyara su tare da tabbatar da ganin sun dawo sun ci gaba da aiki yadda ya kamata.

“Akwai shirye-shiryen da ake yi na horas da jami’ai ta yadda za su tafi daidai da zamanin, sannan yanzu haka duniya na tafiya ne tare da kwarewar zamani”, in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

Haka zalika, ya bukaci jami’an da aka horas a cibiyoyin da su yi amfani da ilimin da suka samu wajen tabbatar da yin amfani da injinan yadda ake bukata. Sannan ya kuma hore su da su yi amfani da ilimin da suka samu wajen tsayuwa da kafafunsu.

Da suke yin nasu jawabin, mahalarta taron na Kananan Hukumomin da ban da ban sun bayyana cewa, injinan za su iya fitar da balabalan kwallon kafar akalla kimanin guda 100 a kowace rana. Sun kuma kara da cewa, dukkanin Kananan Hukumomin Jihar 44, sun amfani da wadannan cibiyoyi.

Sannan sun kuma roki Gwamnan Jihar, ya samar musu da muhallai na dindindin domin taimaka musu wajen kara jajircewa tare da jan damarar yin aiki yadda ya kamata.

Haka zalika, ababen da kwamishinan ya duba yayin ziyarar tasa sun hada da injin yanka kwallon kafa da jannareto mai girman 15KBA da kuma fatar da ake yin amfani da ita wajen lullebe kwallon da kuma wasu sauran kayayyaki.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

April 19, 2025
Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

March 8, 2025
Next Post
Mutum 30 Sun Halaka Tare Da Sace Mutum 19 A Abuja

'Yan Bindiga Sun Kutsa Kai Jami'ar Tarayya Ta Gusau Sun Sace Dalibai

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
katsina

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

October 17, 2025
Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

October 17, 2025
Abduljabbar

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

October 17, 2025
An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

October 17, 2025
Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

October 17, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.