ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kano Ta Rungumi Ilimin Kimiyya Don Kyautata Rayuwar Jama’a – Kwamishina

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Kano

Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana aniyarta ta rungumar harkokin kimiyya da fahasa, domin kyautata rayuwar dumbin al’ummar da ke fadin jihar ta hanyar bayar da muhimmanci ga harkokin kimiyya da fasaha a jihar.

Kwamishinan Ma’aikatar Kimiyya, fasaha da kere-keren zamani na jihar, Muhammed Tajo Othman, wanda ya jagoranci babban sakatare da daraktocin ma’aikatar zuwa zagayen duba Cibiyar Musulunci ta Kura da Wudil da suke jihar, domin duba injinan wasan kwallon kafa da wasu injinan da aka yi watsi da su.

  • Ganduje Ya Magantu Kan Nasarar Jam’iyyar APC A Kano, Ya Ce Gawuna Zai Zo Wa Kano Da Alheri

Tajo Othman ya ce, Gwamnatin Alhaji Abba Kabir Yusuf, ta sanya hankali sosai wajen ganin ta yi amfani da harkokin kimiyya da fasaha da kere-kere, domin tabbatar da cewa a halin da ake ciki yanzu na kimiyya da fasaha na taimakawa sosai wajen bukatar ci gaba, don haka jihar ba za ta yi wasa da wannan fanni ko kadan ba.

ADVERTISEMENT

Kwamishinan ya kara dacewa, ziyarar na kunshe ne da manufar duba halin da injinan suke ciki, domin ganin an bi matakan da suka dace wajen gyara su tare da tabbatar da ganin sun dawo sun ci gaba da aiki yadda ya kamata.

“Akwai shirye-shiryen da ake yi na horas da jami’ai ta yadda za su tafi daidai da zamanin, sannan yanzu haka duniya na tafiya ne tare da kwarewar zamani”, in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Haka zalika, ya bukaci jami’an da aka horas a cibiyoyin da su yi amfani da ilimin da suka samu wajen tabbatar da yin amfani da injinan yadda ake bukata. Sannan ya kuma hore su da su yi amfani da ilimin da suka samu wajen tsayuwa da kafafunsu.

Da suke yin nasu jawabin, mahalarta taron na Kananan Hukumomin da ban da ban sun bayyana cewa, injinan za su iya fitar da balabalan kwallon kafar akalla kimanin guda 100 a kowace rana. Sun kuma kara da cewa, dukkanin Kananan Hukumomin Jihar 44, sun amfani da wadannan cibiyoyi.

Sannan sun kuma roki Gwamnan Jihar, ya samar musu da muhallai na dindindin domin taimaka musu wajen kara jajircewa tare da jan damarar yin aiki yadda ya kamata.

Haka zalika, ababen da kwamishinan ya duba yayin ziyarar tasa sun hada da injin yanka kwallon kafa da jannareto mai girman 15KBA da kuma fatar da ake yin amfani da ita wajen lullebe kwallon da kuma wasu sauran kayayyaki.

Kano
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC

MASU ALAKA

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya

February 21, 2026
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

April 19, 2025
Next Post
Mutum 30 Sun Halaka Tare Da Sace Mutum 19 A Abuja

'Yan Bindiga Sun Kutsa Kai Jami'ar Tarayya Ta Gusau Sun Sace Dalibai

LABARAI MASU NASABA

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Tattaunawar Neman Aiki…

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Tattaunawar Neman Aiki…

June 8, 2026
Morocco Na Fargabar Rashin Ƴan Wasa 2 Gabanin Karawa Da Brazil

Morocco Na Fargabar Rashin Ƴan Wasa 2 Gabanin Karawa Da Brazil

June 8, 2026
Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance

Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance

June 8, 2026
Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

June 8, 2026
Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

June 8, 2026
Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta

Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta

June 8, 2026
Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

June 8, 2026
An Ceto Mutane 360 Daga Hannun Boko Haram, Wasu Na Can Riƙe Wurinsu

An Ceto Mutane 360 Daga Hannun Boko Haram, Wasu Na Can Riƙe Wurinsu

June 8, 2026
Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

June 7, 2026
A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

June 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.