• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’an Tsaro Da ‘Yan Sintiri Sun Yi Nasarar Halaka ‘Yan Bindiga A Jihar Kebbi

by Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
Mutum 30 Sun Halaka Tare Da Sace Mutum 19 A Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’an tsaron hadin vuiwa da wasu ‘yan sintiri sun yi nasarar halaka wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne guda 21 a karamar hukumar Danko Wasagu a jihar Kebbi.

Shugaban karamar hukumar, Alhaji Hussani Aliyu-Bena, ya bayyana cewa, jami’an sun yi wannan nasarar ne a ranar Laraba.

  • Harin ‘Yan Bindiga A Kauyen Dan-Umaru: ‘Yansanda Sun Kwato Roka A Kebbi
  • ‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 4 Tare Da Cafke 9 A Jihar Kaduna.

A cewarsa, an kashe su ne a lokacin da suke shirin tsallaka wa jihar Kebbi, ta hanyar da ta taso daga yankin Mariga da ke a jihar Neja, inda jami’an suka yi masu kwanton bauna a yankin Tudun Bichi suka kuma samu nasarar hallaka su.

Shugaban ya ci gaba da cewa, Wasagu ta yi iyaka ne da Mariga da ke a jihar Neja wadda ta zamo wa ‘yan bindigar hanya mafi sauki da suke yin amfani da ita don shiga cikin yankunan da ke cikin jihar Kebbi.

Kazalika, ya bayyana cewa, ‘yan bindigar sun kuma kashe Marafan Mai Inuwa, da ke a karkashin gundumar Kanya tare da sace wasu mutane, amma daga baya, soji suka ceto su, suka kashe wasu daga cikin ‘yan bindigar.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

Ya bukaci da a kara tura yawan jami’an tsaro zuwa yankunan Malekachi da Dankade, ganin cewa, ‘yan bindigar na yin amfani da hanyoyin wadannan yankunan don wucewa.

Shugaban, ya yabawa jami’ai kan wannan namijin kokarin na halaka ‘yan bindigar.

A cewars, bisa umarnin gwamanan jihar, Nasiru Idris, ‘yan majalisar karamar hukumar sun kai ziyara gundumar ta Kanya, wajen da alummar da ‘yan bindiga suka raba su da matsagunansu suka taru a nan.

Sai dai har zuwa lokacin hada wannan rahoton, Kakakin rundunar ‘Yansandan jihar, SP Nafiu Abubakar, bai fitar da wata sanarwa kan wannab lamarin ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KebbiYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ga MDD: Afirka Ta Gaji Da Kashin Dankali

Next Post

Kano Ta Rungumi Ilimin Kimiyya Don Kyautata Rayuwar Jama’a – Kwamishina

Related

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

26 minutes ago
Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet
Labarai

Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

8 hours ago
Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya
Ra'ayi Riga

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

13 hours ago
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa
Labarai

Abba Ya Yi Sabbin Naɗe-naɗe A Jihar Kano

14 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

14 hours ago
Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari
Labarai

Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari

14 hours ago
Next Post
Kano Ta Rungumi Ilimin Kimiyya Don Kyautata Rayuwar Jama’a – Kwamishina

Kano Ta Rungumi Ilimin Kimiyya Don Kyautata Rayuwar Jama’a - Kwamishina

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

July 5, 2025
In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

July 4, 2025
Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

July 4, 2025
Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

July 4, 2025
Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

July 4, 2025
Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

July 4, 2025
Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

July 4, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

July 4, 2025
Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

July 4, 2025
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

July 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.