• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Martanin Da Ya Biyo Bayan Hukuncin Kotun Zaben Gwamnonin Kano, Bauchi Da Zamfara 

by Sadiq, Khalid Idris Doya and Hussein Yero
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Kotu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wannan makon ne kutunan sauraron kararrakin zaben gwamnoni suka zartar da hukunci a Jihohin Kano, Bauchi da kuma Zamfara, lamarin da ya janyo martani Sai daban-daban kan hukunce-hukuncen kotun.  

A ranar Laraba kotun sauraren kararrakin zabe ta zartar da hukunci kan zaben Gwamnan Jihar Kano da aka yi a ranar 18 ga watan Maris, 2023.

  • Mataimakin Gwamnan Jihar Edo, Shaibu Ya Roki Obaseki Ya Gafarce Shi

Kotun ta kwace kujerar gwamna daga hannun Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP tare da ayyana dan takarar jam’iyyar APC, Nasiru Yusuf Gawuna a matsayin wanda ya lashe zaben.

Sai dai wannan hukunci ya bar baya da kura tare da barin dubban mutane cikin dar-dari da fargabar abin da ka iya zuwa ya dawo.

Tun da fari dai lauyoyin NNPP sun yi fatali da hukuncin kotun, inda suka ce za su daukaka kara. Magoya bayan jam’iyyar NNPP na ganin an yi bita da kulli wajen kwace musu ‘yancinsu.

Labarai Masu Nasaba

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

A gefe daya kuma, magoya bayan jam’iyyar APC sun shiga murna da shewa tare da fitowa kan wasu tituna na jihar don nuna farin cikinsu kan nasarar da suka samu a kotu.

Sai dai kasuwanni irin su Sabon Gari, Kwari, Wambai, Farm centre da sauransu sun rufe shaguna saboda gudun tashin rikici.

Tuni dai kafafen sada zumunta suka dauki dumi, idan magoya bayan duka manyan jam’iyyun adawa suka shiga bayyana ra’ayoyi mabanbanta.

Tun a ranar Talata ne aka girke daruruwan jami’an tsaro a manyan titunan kwaryar Kano, domin shirin ko ta kwana a yayin zartar da hukuncin.

Da safiyar ranar Laraba ne jagororin kowace jam’iyya suka isa harabar kotun don jin hukuncin da kotun za ta zartar karkashin jagorancin alkali, Oluyemi Akintan-Osadebay.

Sai dai daga bisani aka bayyana cewar za a zartar da hukuncin ne ta Intanet ta hanyar amfani da manhajar ‘Zoom’. A gefe guda kuwa, jami’an tsaro na ci gaba da tabbatar da doka da oda a jihar.

Haka zalika, kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan Jihar Bauchi a ranar Laraba ta tabbatar da nasarar Bala Muhammad a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna a 2023 da ya gudana, inda ta kori karar da dan takarar jam’iyyar APC Sadikue Abubakar ya shigar da ke kalubalantar nasarar Bala. Sai dai kotun ta ce karar bai da madogara don haka ta kori korafin.

Gwamnna Bala ya misalta nasarar da ya samu daga Allah ne, don haka ya nuna matukar godiyarsa a bisa sake zabinsa da al’ummar jihar suka yi a karo na biyu.

Da yake ganawa da ‘yan jarida bayan tabbatar da nasarar, Bala Muhammad ya ce dimukuradiyya ce ta yi halinta, kuma hakan zai kara masa himma da azama wajen ganin ya ci gaba da yin kokarinsa domin sabunta Jihar Bauchi.

Ya nemi hadin guiwar masu ruwa da tsaki ciki har da abokan hamayyarsa da su zo a hada karfi da karfe domin ciyar da Jihar Bauchi gaba.

Da yake nuna farin cikinsa bisa wannan nasarar, Kakakin Majalisar dokokin Jihar Bauchi, Abubakar Y Sulaiman ya nuna gayar farin cikinsa bisa nasarar da Bala Muhammad ya samu a kotun sauraron kararrakin zaben.

A wata sanarwa da mai Magana da yawunsa, Abdul Ahmed Burra ya fitar, Abubakar ya nemi al’ummar jihar da su ci gaba da mara wa gwamnati da majalisar dokokin jihar baya domin sauke nauyin da ke gabansu.

Daya daga cikin kwamitin yada labarai na dan takarar APC da ya nemi a sakaya sunansa, ya shaida wa wakilinmu cewa suna kan nazarta hukuncin domin daukan mataki na gaba.

“Muna kan nazartar hukuncin kuma in sha Allah za a dauki matakin da ya dace cikin gaggawa,” ya shaida.

A bangare guda kuma, kotun sauraran kara ta zabe da ke zamanta a Sakkwato ta tabbatar da nasarar Gwamna Dauda Lawal a matsayin gwamnan Jihar Zamfara.

Al’umma jihar da suka zanta da wakilinmu kan hukuncin, sun bayyana ra’ayoyinsu.

Muhamda Gali ya bayyana cewa gaskiya ce ta yi halinta tun da zabe da aka yi wa gwamna Dauda a bayyane yake babu magudi a zabensa, wanda bai da gwamnatin yaya zai yi magudi.

A cewarsa, jamiyyar APC ta yi hakuri a wannan karon, domin PDP Allah ya tabbatar mata da mulki, kuma wannan ya ishi mutane ishara.

Shi kuwa wani dan jamiyyar APC da ya nemi na sakaya sunansa ya bayyana cewa, “Mu ne muka jawo wa kanmu faduwar zabe, saboda irin kalamun da muke furtawa na cewa tun da ga Matawale ga Shehi dole ne mu ci zabe ba tare da fadin in sha Allah ba, sai gashi Allah ya jarra be mu da rashin cin zaben.

“Allah ya nuna mana ishara. Domin haka, dole jamiyyar APC ta hakura zuwa wani zaben mai zuwa.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BauchikanoKotun sauraron kararrakin zabeNNPPZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Han Zheng Ya Bukaci Kasashen Duniya Su Ci Gaba Da Bin Tsarin Bangarori Daban-daban Da Kyautata Tsarin Shugabancin Duniya

Next Post

Han Zheng: A Shirye Sin Take Ta Inganta Hadin Gwiwa Da Saliyo 

Related

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

4 days ago
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

2 weeks ago
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa
Tambarin Dimokuradiyya

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

2 weeks ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

1 month ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

1 month ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

1 month ago
Next Post
Han Zheng: A Shirye Sin Take Ta Inganta Hadin Gwiwa Da Saliyo 

Han Zheng: A Shirye Sin Take Ta Inganta Hadin Gwiwa Da Saliyo 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Katsina Ya Dawo Gida Domin Ziyara Ga Al’ummar Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Malumfashi

Gwamnan Katsina Ya Dawo Gida Domin Ziyara Ga Al’ummar Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Malumfashi

August 27, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

August 27, 2025
Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

August 27, 2025
Nijeriya Za Ta Ɗaukaka Da Fasahar Ƙere-ƙere Da Tattalin Abinci – Tinubu

Nijeriya Za Ta Ɗaukaka Da Fasahar Ƙere-ƙere Da Tattalin Abinci – Tinubu

August 27, 2025
Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

August 27, 2025
Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

August 27, 2025
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.