ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Martanin Da Ya Biyo Bayan Hukuncin Kotun Zaben Gwamnonin Kano, Bauchi Da Zamfara 

by Sadiq, Khalid Idris Doya and Hussein Yero
3 years ago
Kotu

A wannan makon ne kutunan sauraron kararrakin zaben gwamnoni suka zartar da hukunci a Jihohin Kano, Bauchi da kuma Zamfara, lamarin da ya janyo martani Sai daban-daban kan hukunce-hukuncen kotun.  

A ranar Laraba kotun sauraren kararrakin zabe ta zartar da hukunci kan zaben Gwamnan Jihar Kano da aka yi a ranar 18 ga watan Maris, 2023.

  • Mataimakin Gwamnan Jihar Edo, Shaibu Ya Roki Obaseki Ya Gafarce Shi

Kotun ta kwace kujerar gwamna daga hannun Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP tare da ayyana dan takarar jam’iyyar APC, Nasiru Yusuf Gawuna a matsayin wanda ya lashe zaben.

ADVERTISEMENT

Sai dai wannan hukunci ya bar baya da kura tare da barin dubban mutane cikin dar-dari da fargabar abin da ka iya zuwa ya dawo.

Tun da fari dai lauyoyin NNPP sun yi fatali da hukuncin kotun, inda suka ce za su daukaka kara. Magoya bayan jam’iyyar NNPP na ganin an yi bita da kulli wajen kwace musu ‘yancinsu.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

A gefe daya kuma, magoya bayan jam’iyyar APC sun shiga murna da shewa tare da fitowa kan wasu tituna na jihar don nuna farin cikinsu kan nasarar da suka samu a kotu.

Sai dai kasuwanni irin su Sabon Gari, Kwari, Wambai, Farm centre da sauransu sun rufe shaguna saboda gudun tashin rikici.

Tuni dai kafafen sada zumunta suka dauki dumi, idan magoya bayan duka manyan jam’iyyun adawa suka shiga bayyana ra’ayoyi mabanbanta.

Tun a ranar Talata ne aka girke daruruwan jami’an tsaro a manyan titunan kwaryar Kano, domin shirin ko ta kwana a yayin zartar da hukuncin.

Da safiyar ranar Laraba ne jagororin kowace jam’iyya suka isa harabar kotun don jin hukuncin da kotun za ta zartar karkashin jagorancin alkali, Oluyemi Akintan-Osadebay.

Sai dai daga bisani aka bayyana cewar za a zartar da hukuncin ne ta Intanet ta hanyar amfani da manhajar ‘Zoom’. A gefe guda kuwa, jami’an tsaro na ci gaba da tabbatar da doka da oda a jihar.

Haka zalika, kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan Jihar Bauchi a ranar Laraba ta tabbatar da nasarar Bala Muhammad a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna a 2023 da ya gudana, inda ta kori karar da dan takarar jam’iyyar APC Sadikue Abubakar ya shigar da ke kalubalantar nasarar Bala. Sai dai kotun ta ce karar bai da madogara don haka ta kori korafin.

Gwamnna Bala ya misalta nasarar da ya samu daga Allah ne, don haka ya nuna matukar godiyarsa a bisa sake zabinsa da al’ummar jihar suka yi a karo na biyu.

Da yake ganawa da ‘yan jarida bayan tabbatar da nasarar, Bala Muhammad ya ce dimukuradiyya ce ta yi halinta, kuma hakan zai kara masa himma da azama wajen ganin ya ci gaba da yin kokarinsa domin sabunta Jihar Bauchi.

Ya nemi hadin guiwar masu ruwa da tsaki ciki har da abokan hamayyarsa da su zo a hada karfi da karfe domin ciyar da Jihar Bauchi gaba.

Da yake nuna farin cikinsa bisa wannan nasarar, Kakakin Majalisar dokokin Jihar Bauchi, Abubakar Y Sulaiman ya nuna gayar farin cikinsa bisa nasarar da Bala Muhammad ya samu a kotun sauraron kararrakin zaben.

A wata sanarwa da mai Magana da yawunsa, Abdul Ahmed Burra ya fitar, Abubakar ya nemi al’ummar jihar da su ci gaba da mara wa gwamnati da majalisar dokokin jihar baya domin sauke nauyin da ke gabansu.

Daya daga cikin kwamitin yada labarai na dan takarar APC da ya nemi a sakaya sunansa, ya shaida wa wakilinmu cewa suna kan nazarta hukuncin domin daukan mataki na gaba.

“Muna kan nazartar hukuncin kuma in sha Allah za a dauki matakin da ya dace cikin gaggawa,” ya shaida.

A bangare guda kuma, kotun sauraran kara ta zabe da ke zamanta a Sakkwato ta tabbatar da nasarar Gwamna Dauda Lawal a matsayin gwamnan Jihar Zamfara.

Al’umma jihar da suka zanta da wakilinmu kan hukuncin, sun bayyana ra’ayoyinsu.

Muhamda Gali ya bayyana cewa gaskiya ce ta yi halinta tun da zabe da aka yi wa gwamna Dauda a bayyane yake babu magudi a zabensa, wanda bai da gwamnatin yaya zai yi magudi.

A cewarsa, jamiyyar APC ta yi hakuri a wannan karon, domin PDP Allah ya tabbatar mata da mulki, kuma wannan ya ishi mutane ishara.

Shi kuwa wani dan jamiyyar APC da ya nemi na sakaya sunansa ya bayyana cewa, “Mu ne muka jawo wa kanmu faduwar zabe, saboda irin kalamun da muke furtawa na cewa tun da ga Matawale ga Shehi dole ne mu ci zabe ba tare da fadin in sha Allah ba, sai gashi Allah ya jarra be mu da rashin cin zaben.

“Allah ya nuna mana ishara. Domin haka, dole jamiyyar APC ta hakura zuwa wani zaben mai zuwa.”

Zabe
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
Zabe
Hussein Yero
+ posts Bio
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    ’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Ɗan Takarar Sanata A Zamfara Ya Koka Kan Yi Wa Rayuwarsa Barazana
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Abdulaziz Yari Ya Bukaci Limamai Su Ƙara Addu’a Kan Yaƙi Da Ƴan Bindiga A Zamfara

MASU ALAKA

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Next Post
Han Zheng: A Shirye Sin Take Ta Inganta Hadin Gwiwa Da Saliyo 

Han Zheng: A Shirye Sin Take Ta Inganta Hadin Gwiwa Da Saliyo 

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.