• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamnatin Tinubu Ta Shirya Tsara ‘Yan Nijeriya Da Farfaganda – Atiku

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya, Manyan Labarai
0
Atiku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP kuma tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya yi zargin cewa, gwamnatin Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu ta shirya tsara ‘yan Nijeriya a wasu kwanaki masu zuwa. 

Ya bayyana cewa Tinubu ya nada masu ba shi sharawa a kan fannin yada labarai sama da 15, saboda su dunga fitar da bayanai marasa inganci kan manufofi gwamnati tare da kawar da hankalin ‘yan Nijeriya kan matsanancin halin da gwamnatinsa ta jefa su a ciki.

  • Bayan Gindaya Wa’adi: Hukumar AGIS Na Tattara Harajin Naira Biliyan Daya A Kullum 

A cikin wata sanarwa da mataimaki na musamman kan harkokin sadarwa, Phrank Shaibu, ya ce labarin karya ne ake yadawa game da dage haramcin biza da kasar Dubai ta yi wa Nijeriya, amma babu kamshin gaskiya cikin lamarin.

Ya ce wannan shi ne salon gwamnatin Tinubu kuma shugaban jam’iyyarsa.

Atiku ya ce, “Daga bayanan da muka samu, Bola Tinubu na shirin tura farfaganda don wuce gona da iri yayin da yake shirin halartar taron Majalisar Dinkin Duniya. Zai yi ikirarin ya janyo masu zuba jari na kasashen waje da ya kai dala biliyan 100, amma zai kasa bayar da cikakkun bayanai. Wannan duk farfaganda ce. A kasar Indiya, ya yi ikirarin cewa sun karbi hannun jari sama da dala biliyan 14 kamar yadda magabacinsa, tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi a shekarar 2018 cewa ya karbi na dala biliyan 6. Wannan ba komai ba ne illa saka hannun jari na fatar baki.

Labarai Masu Nasaba

Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

“A watan da ya gabata, kamfanin NNPC ya yi ikirarin cewa ya samu rancen dala biliyan 3 da zai taimaka wajen daidaita darajar naira. Mun bayyana cewa duk wannan wata dabara ce ta yaudarar ‘yan Nijeriya. Yanzu dai mun tabbatar da cewa naira na kara durkushewa, wanda a yanzu haka dala ta kusan naira1,000 a kasuwar bayan fage.

“Bayan tafiyarsa zuwa Dubai, Tinubu ya yi ikirarin cewa an dage takunkumin haramcin biza nan take. Yanzu haka sun sauya sheka bayan da hukumomin kasar Dubai suka bayyana cewa labarin karya ne. Irin wannan abin kunya ne ga Nijeriya wanda gwamnati ke ci gaba da jawowa a wannan mulki.

“Duk da ya kasa inganta harkokin tattalin arzikin kasa, amma ya nada masu ba shi shawara kan harkokin yada labarai har guda 15, maimakon ya nada masana tattalin arziki.

“Daga cikin jerin masu ba shi shawara kan harkokin yada labarai akwai da sadarwa akwai: Tunde Rahman,Tope Ajayi, Abdulaziz Abdulaziz, Otega Ogara, Segun Dada da Nosa Asemota .

Sauran su ne: Sunday Moses, Taiwo Okonlawon, Moremi Ojudu, Tanko Yakasai, Chioma Nweze, Abiodun Essiet, Abdulhamid Yahaya Abba da kuma Emmanuella Eduozor. Baya ga wadannan akwai kuma ministan yada labarai da suran wasu nade-nade a ma’aikatan domin yada farfaganda.”

Ya bukaci ‘yan Nijeriya su ci gaba da hakuri a daidai lokacin da kotun koli ke shirin zantar da hukunci kan zaben shugaban kasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCAtikuPDPSiyasaTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bunkasa Kimiyya Da Fasaha: Nijeriya Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasar Cuba

Next Post

Cristiano Ronaldo Ya Zura Kwallaye Uku Rigis A Wasansu Da Al Ahl

Related

Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang
Manyan Labarai

Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

2 hours ago
David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC
Manyan Labarai

David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

4 hours ago
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano
Manyan Labarai

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

17 hours ago
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

22 hours ago
Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata
Manyan Labarai

Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

1 day ago
Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama
Manyan Labarai

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

1 day ago
Next Post
Cristiano Ronaldo Ya Zura Kwallaye Uku Rigis A Wasansu Da Al Ahl

Cristiano Ronaldo Ya Zura Kwallaye Uku Rigis A Wasansu Da Al Ahl

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea

Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea

July 2, 2025
Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

July 2, 2025
David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

July 2, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sake Kashe Mutum 6 A Ƙauyukan Filato, Sun Jikkata Wasu

Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato

July 2, 2025
An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.