• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamnatin Tinubu Ta Shirya Tsara ‘Yan Nijeriya Da Farfaganda – Atiku

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya, Manyan Labarai
0
Atiku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP kuma tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya yi zargin cewa, gwamnatin Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu ta shirya tsara ‘yan Nijeriya a wasu kwanaki masu zuwa. 

Ya bayyana cewa Tinubu ya nada masu ba shi sharawa a kan fannin yada labarai sama da 15, saboda su dunga fitar da bayanai marasa inganci kan manufofi gwamnati tare da kawar da hankalin ‘yan Nijeriya kan matsanancin halin da gwamnatinsa ta jefa su a ciki.

  • Bayan Gindaya Wa’adi: Hukumar AGIS Na Tattara Harajin Naira Biliyan Daya A Kullum 

A cikin wata sanarwa da mataimaki na musamman kan harkokin sadarwa, Phrank Shaibu, ya ce labarin karya ne ake yadawa game da dage haramcin biza da kasar Dubai ta yi wa Nijeriya, amma babu kamshin gaskiya cikin lamarin.

Ya ce wannan shi ne salon gwamnatin Tinubu kuma shugaban jam’iyyarsa.

Atiku ya ce, “Daga bayanan da muka samu, Bola Tinubu na shirin tura farfaganda don wuce gona da iri yayin da yake shirin halartar taron Majalisar Dinkin Duniya. Zai yi ikirarin ya janyo masu zuba jari na kasashen waje da ya kai dala biliyan 100, amma zai kasa bayar da cikakkun bayanai. Wannan duk farfaganda ce. A kasar Indiya, ya yi ikirarin cewa sun karbi hannun jari sama da dala biliyan 14 kamar yadda magabacinsa, tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi a shekarar 2018 cewa ya karbi na dala biliyan 6. Wannan ba komai ba ne illa saka hannun jari na fatar baki.

Labarai Masu Nasaba

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu

Shettima Ya Ziyarci Buhari A Landan Cikin Sirri Don Duba Lafiyarsa

“A watan da ya gabata, kamfanin NNPC ya yi ikirarin cewa ya samu rancen dala biliyan 3 da zai taimaka wajen daidaita darajar naira. Mun bayyana cewa duk wannan wata dabara ce ta yaudarar ‘yan Nijeriya. Yanzu dai mun tabbatar da cewa naira na kara durkushewa, wanda a yanzu haka dala ta kusan naira1,000 a kasuwar bayan fage.

“Bayan tafiyarsa zuwa Dubai, Tinubu ya yi ikirarin cewa an dage takunkumin haramcin biza nan take. Yanzu haka sun sauya sheka bayan da hukumomin kasar Dubai suka bayyana cewa labarin karya ne. Irin wannan abin kunya ne ga Nijeriya wanda gwamnati ke ci gaba da jawowa a wannan mulki.

“Duk da ya kasa inganta harkokin tattalin arzikin kasa, amma ya nada masu ba shi shawara kan harkokin yada labarai har guda 15, maimakon ya nada masana tattalin arziki.

“Daga cikin jerin masu ba shi shawara kan harkokin yada labarai akwai da sadarwa akwai: Tunde Rahman,Tope Ajayi, Abdulaziz Abdulaziz, Otega Ogara, Segun Dada da Nosa Asemota .

Sauran su ne: Sunday Moses, Taiwo Okonlawon, Moremi Ojudu, Tanko Yakasai, Chioma Nweze, Abiodun Essiet, Abdulhamid Yahaya Abba da kuma Emmanuella Eduozor. Baya ga wadannan akwai kuma ministan yada labarai da suran wasu nade-nade a ma’aikatan domin yada farfaganda.”

Ya bukaci ‘yan Nijeriya su ci gaba da hakuri a daidai lokacin da kotun koli ke shirin zantar da hukunci kan zaben shugaban kasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCAtikuPDPSiyasaTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bunkasa Kimiyya Da Fasaha: Nijeriya Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasar Cuba

Next Post

Cristiano Ronaldo Ya Zura Kwallaye Uku Rigis A Wasansu Da Al Ahl

Related

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu
Manyan Labarai

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu

17 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Shettima Ya Ziyarci Buhari A Landan Cikin Sirri Don Duba Lafiyarsa

18 hours ago
Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa
Kotu Da Ɗansanda

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

20 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Lauyoyin Natasha Sun Buƙaci Ta Koma Majalisa Ranar Talata Bayan Miƙa Takardun Hukuncin Kotu

20 hours ago
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Tambarin Dimokuradiyya

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

24 hours ago
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

1 day ago
Next Post
Cristiano Ronaldo Ya Zura Kwallaye Uku Rigis A Wasansu Da Al Ahl

Cristiano Ronaldo Ya Zura Kwallaye Uku Rigis A Wasansu Da Al Ahl

LABARAI MASU NASABA

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

July 12, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

July 12, 2025
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

July 12, 2025
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

July 12, 2025
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

July 12, 2025
Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.