• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Na Kara Kwarjini A Idon Duniya Karkashin Tinubu – Ministan Labarai

by Abdulrazaq Yahuza
2 years ago
Ministan Labarai

Ministan Labarai na Nijeriya, Mohammed Idris Malagi, ya bayyana cewa, Nijeriya na kara kwarjini samun tagomashi da kwarjini a idon duniya karkashin kyakkyawan jagorancin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu yake bai wa kasar.

Ministan Labaran ya bayyana hakan ne jiya a tattaunawar da ya yi da Gidan Talabijin na Nijeriya (NTA) a Babban Taron Majalisar dinkin Duniya da ake gudanarwa a New York dake Amurka, inda ya kara da cewa, Shugaban Nijeriyar ya kara fito da martabar ba wai kawai Nijeriya ita kadai ba, a’a, har ma da Nahiyar Afrika bakidaya.

  • Yadda Gwamnatin Tinubu Ta Shirya Tsara ‘Yan Nijeriya Da Farfaganda – Atiku
  • Zargin Daura Aure Da Mai Kanjamau: Yadda Aka Tube Hakimi A Katsina

“Ziyara ce mai matukar ban sha’awa da Shugaban kasar ya gudanar. Ya zo ne ba don Nijeriya kadai ba, amma har ma da Afrika,” inji shi.

“Tabbas kun gan shi (Shugaba Tinubu) tare da Shugaban kasar Afrika ta Kudu, Cyril Ramophosa; kun gan shi da Shugaban Tarayyar Comoros, Shugaba Azali Assoumani, kun gan shi tare da Aaki Hussein na Jordan da Shugaban kasar Angola, inda dukkanninsu suka kasance a shirye suke wajen ganin Nijeriya ta daidaita a inda ta dace da matsayinta.

“daga dukkan alamu duniya tana sake maraba da Nijeriya izuwa ga martabar da ta dace da ita. Abubuwa da dama suna ta faruwa.

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

“Ana sa ido kan Nijeriya don ganin ta yi jagoranci tafiyar, kuma Shugaba Tinubu yana jan ragamar a halin yanzu. Don haka a yanzu Nijeriya tana sake zama muhimmiyar kasa a duniya ta hanyar komawa kan matsayinta da aka san ta da shi.”

Daga nan sai Ministan ya bayar da misali da irin yadda Shugaba Tinubu ya gabatar da tsararre kuma kyakkyawan jawabinsa a gaban Babban Zauren Majalisar Dinkin Duniyar, inda ya tabbatar da tsarin siyasar dimukradiyya a matsayin tsari mafi inganci dake bayar da cikakken ’yanci da jin dadi da walwala ga al’umma da kuma yadda Afrika ke fama da tashe-tashen hankulan masu tsattsauran ra’ayi a nahiyar ta yadda ta janyo hankalin kasashen duniya, don su kawo agaji a yankin.

Daga nan sai Malagi ya yi wa ’yan Nijeriya albishir kan yadda Tinubu ya samu amincewar Kamfanin EddonMobil, wanda ya yi alkawarin samar da makamashi 40,000 a matsayin sabon zuba jari a kasar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

October 16, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara
Labarai

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025
Sabbin Ministoci
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

October 16, 2025
Next Post
Gwamnatin Zamfara

Matsalar Tsaro: Gwamnatin Zamfara Ta Haramta Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba

LABARAI MASU NASABA

Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya

Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya

October 16, 2025
Tinubu

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

October 16, 2025
Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

October 16, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025
Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

October 16, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

October 16, 2025
Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

October 16, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

October 16, 2025
Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.