• English
  • Business News
Wednesday, September 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta Ina Talakawa Za Su Mori Rage Farashin Simintin BUA?

by Bello Hamza
2 years ago
in Labarai
0
BUA
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamar yadda aka sani, kamfanin siminti na BUA karkashin jagorancin Alhaji Abdussamad Rabiu ya sanar da cewa, nan gaba kadan zai rage farashin siminti a fadin kasar daga naira 5,500 a kan kowanne buhu zuwa Naira 3,000. Ya ce, sun yanke wannan shawarar ne don yin haka tamkar nuna goyon bayansu ga kudurin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu na samar da isssun gidaje ga al’umma Nijeriya da kuma hankoron ganin an samar da ayyukan yi ga dinbin matasanmu.

Tabbas wannan shirin zai taikama wa rayuwwar talakan Nijeriya, don samar da siminti mai sauki zai zaburar da harkar kwangila na gine-gine a fadin tarayya Nijeriya abin da kuma zai kai ga daukar masu kananan sana’o’i da leburori da dama aiki.

  • An Gabatar Da Sanarwar Taron Kula Da Harkokin Masana’antu Da Kasuwanci Bisa Doka
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Sabbin Shirye-shiryen Inganta Tsaro A Jihar Kaduna

Babu shakka in har leburori da birkila, da masu walda da fulamba da sauran wadanda suke gudanar da sana’ar su da ta shafi bangaren gine-gine suka samu abin yi, al’umma da suka shafe su za su samu abinci mutane za su samu karin walwala.

Sai dai tambayar da mutane da dama suke yi, shi ne wai shin yaushe za a fara cin gajiyar wannan rage farashin? Shugaban kamfanin BUA, Alhaji Abudussamad Rabiu ya ce, wannan Shirin ya danganta ne ga shirinnsu na bude wasu sabbin kamfanoni biyu da suke sa ran za su rinka samar da tan miliyan 3 na siminti a duk mshekara wanda suke sa ran za a kamala aikin ginawa nan zuwa karshen shekara.

Sabbin kamfanonin guda biyu in har suka fara aikii za su kara yawan simintin da BUA ke samarwa zuwa tan Miliyan 17 a duk shekara wanda hakan zai mayar da kamfanin mafi girma a bangaren samar da siminti a fadin Afirka gaba daya. Shugaban kamfanin ya ce, suna sa ran cimma wanna ne saboda yadda suke samar da kayan hada simininti a cikin gida.

Labarai Masu Nasaba

An Ɗauke Wuta Sakamakon Lalacewar Babbar Tashar Lantarkin Nijeriya

Gwamnatin Kaduna Ta Umarci Makarantu Masu Zaman Kansu Da Su Nemi Amincewarta Kafin Ƙara Kuɗi

“Kashi 80 na kayan da muke hada siminti da su muna samu ne daga cikin gida, a kan haka muke son tallafa wa gwamnati wajen tabbatar da ganin an dawo da farashin siminti zuwa farashin da ya dace da talaka.” In ji shi.

Abdussamad Rabiu ya kuma bayyana cewa, ana sa ran shugaban kasa Tinubu zai kaddamar da sabbin kamfanin nan gaba a cikin wannan shekarar ta yadda abin da muke samarwa zai kai tan miliyan 17 a duk shekara.

Masu sharhi a kan harkokin yau da kullum sun nuna jin dadinsu a kan wannan matakin suna mai cewa, yin hakan zai zaburar da tattalin arzikin kasa, musamman a bangaren gine-gine na kamfanoni da mutane daidaiku.
Wannan ragin kuma zai taimaki al’umma musamman masu gidaje da masu haya don zai kai ga rage kudin haya a nan gaba.
Kotu Da “yansanda


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BUADangote
ShareTweetSendShare
Previous Post

Matakan Fara Sana’ar Hakar Ma’adanai Bisa Doka A Nijeriya

Next Post

Ɗaliban Musawa Da Matazu Za Su Amfana Da Tallafin Karatun Naira Miliyan 32,500 A Katsina

Related

An Ɗauke Wuta Sakamakon Lalacewar Babbar Tashar Lantarkin Nijeriya
Manyan Labarai

An Ɗauke Wuta Sakamakon Lalacewar Babbar Tashar Lantarkin Nijeriya

3 minutes ago
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamnatin Kaduna Ta Umarci Makarantu Masu Zaman Kansu Da Su Nemi Amincewarta Kafin Ƙara Kuɗi

2 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Yadda Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Yaya Da Ƙannuwa Da Wasu A Zaria

3 hours ago
Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027
Manyan Labarai

Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027

4 hours ago
Akwai Tara Mai Tsauri Ga Duk Wanda Ya Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba – Gwamnatin Kano
Labarai

Akwai Tara Mai Tsauri Ga Duk Wanda Ya Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba – Gwamnatin Kano

6 hours ago
majalisar kasa
Manyan Labarai

Majalisa Ta Bai Wa Minista Sa’o’i 48 Ya Bayyana A Gabanta Kan Hatsarin Jirgin Abuja Zuwa Kaduna

8 hours ago
Next Post
Ɗaliban Musawa Da Matazu Za Su Amfana Da Tallafin Karatun Naira Miliyan 32,500 A Katsina

Ɗaliban Musawa Da Matazu Za Su Amfana Da Tallafin Karatun Naira Miliyan 32,500 A Katsina

LABARAI MASU NASABA

An Ɗauke Wuta Sakamakon Lalacewar Babbar Tashar Lantarkin Nijeriya

An Ɗauke Wuta Sakamakon Lalacewar Babbar Tashar Lantarkin Nijeriya

September 10, 2025
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamnatin Kaduna Ta Umarci Makarantu Masu Zaman Kansu Da Su Nemi Amincewarta Kafin Ƙara Kuɗi

September 10, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Yadda Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Yaya Da Ƙannuwa Da Wasu A Zaria

September 10, 2025
Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027

Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027

September 10, 2025
Akwai Tara Mai Tsauri Ga Duk Wanda Ya Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba – Gwamnatin Kano

Akwai Tara Mai Tsauri Ga Duk Wanda Ya Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba – Gwamnatin Kano

September 10, 2025
majalisar kasa

Majalisa Ta Bai Wa Minista Sa’o’i 48 Ya Bayyana A Gabanta Kan Hatsarin Jirgin Abuja Zuwa Kaduna

September 10, 2025
Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

September 9, 2025
IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

September 9, 2025
An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

September 9, 2025
Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

September 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.