ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta Ina Talakawa Za Su Mori Rage Farashin Simintin BUA?

by Bello Hamza
3 years ago
BUA

Kamar yadda aka sani, kamfanin siminti na BUA karkashin jagorancin Alhaji Abdussamad Rabiu ya sanar da cewa, nan gaba kadan zai rage farashin siminti a fadin kasar daga naira 5,500 a kan kowanne buhu zuwa Naira 3,000. Ya ce, sun yanke wannan shawarar ne don yin haka tamkar nuna goyon bayansu ga kudurin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu na samar da isssun gidaje ga al’umma Nijeriya da kuma hankoron ganin an samar da ayyukan yi ga dinbin matasanmu.

Tabbas wannan shirin zai taikama wa rayuwwar talakan Nijeriya, don samar da siminti mai sauki zai zaburar da harkar kwangila na gine-gine a fadin tarayya Nijeriya abin da kuma zai kai ga daukar masu kananan sana’o’i da leburori da dama aiki.

  • An Gabatar Da Sanarwar Taron Kula Da Harkokin Masana’antu Da Kasuwanci Bisa Doka
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Sabbin Shirye-shiryen Inganta Tsaro A Jihar Kaduna

Babu shakka in har leburori da birkila, da masu walda da fulamba da sauran wadanda suke gudanar da sana’ar su da ta shafi bangaren gine-gine suka samu abin yi, al’umma da suka shafe su za su samu abinci mutane za su samu karin walwala.

ADVERTISEMENT

Sai dai tambayar da mutane da dama suke yi, shi ne wai shin yaushe za a fara cin gajiyar wannan rage farashin? Shugaban kamfanin BUA, Alhaji Abudussamad Rabiu ya ce, wannan Shirin ya danganta ne ga shirinnsu na bude wasu sabbin kamfanoni biyu da suke sa ran za su rinka samar da tan miliyan 3 na siminti a duk mshekara wanda suke sa ran za a kamala aikin ginawa nan zuwa karshen shekara.

Sabbin kamfanonin guda biyu in har suka fara aikii za su kara yawan simintin da BUA ke samarwa zuwa tan Miliyan 17 a duk shekara wanda hakan zai mayar da kamfanin mafi girma a bangaren samar da siminti a fadin Afirka gaba daya. Shugaban kamfanin ya ce, suna sa ran cimma wanna ne saboda yadda suke samar da kayan hada simininti a cikin gida.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

“Kashi 80 na kayan da muke hada siminti da su muna samu ne daga cikin gida, a kan haka muke son tallafa wa gwamnati wajen tabbatar da ganin an dawo da farashin siminti zuwa farashin da ya dace da talaka.” In ji shi.

Abdussamad Rabiu ya kuma bayyana cewa, ana sa ran shugaban kasa Tinubu zai kaddamar da sabbin kamfanin nan gaba a cikin wannan shekarar ta yadda abin da muke samarwa zai kai tan miliyan 17 a duk shekara.

Masu sharhi a kan harkokin yau da kullum sun nuna jin dadinsu a kan wannan matakin suna mai cewa, yin hakan zai zaburar da tattalin arzikin kasa, musamman a bangaren gine-gine na kamfanoni da mutane daidaiku.
Wannan ragin kuma zai taimaki al’umma musamman masu gidaje da masu haya don zai kai ga rage kudin haya a nan gaba.
Kotu Da “yansanda

BUA
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Ɗaliban Musawa Da Matazu Za Su Amfana Da Tallafin Karatun Naira Miliyan 32,500 A Katsina

Ɗaliban Musawa Da Matazu Za Su Amfana Da Tallafin Karatun Naira Miliyan 32,500 A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.