ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matakan Fara Sana’ar Hakar Ma’adanai Bisa Doka A Nijeriya

by Bello Hamza
3 years ago
Ma'adanai

Hakar ma’adanai na da matukar muhimmanci ga tattalin arzikin Nijeriya da ma Afirka gaba daya. Ta nan ne ake samar wa masana’antunmu na ciki da wajen kasa kayan sarrafawa, wanda kuma hakan ke samar da aikin yi ga dimbin matasa a ciki da wajen kasar nan.

A Nijeriya, tarihi ya nuna irin tasirin ma’adanai ga tattalin arzikin kasa inda ake samun fiye da kashi 0.3 na arzikin kasa daga bangaren ma’adanai (kamar yadda bayani ya nuna a kasafin kudin shekarar 2022). Bincike ya kuma nuna cewa, a yankin Afirka ake samun kashi 30 na dukkan ma’adanai na duniya, lamarin da ya sa Afirka a sahun gaba a harkar ma’adanai na duniya.

  • Matsalar Tsaro: Gwamnatin Zamfara Ta Haramta Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba
  • Kotun Sauraren Karar Zaben Gwamna A Legas Za Ta Yanke Hukunci Ranar Litinin

Duk da kasancewar harkar hakar ma’adanai na da muhimmanci ga tattalin arzikin Nijeriya amma har zuwa yanzu ba a kai ga bunkasa sashin ba yadda ya kamata, saboda rashin cikakken kayan aiki na zama da rashin masu zuba jari da kuma yadda har yanzu ake ci gaba da amfani kayan aikin hakar ma’adanai ba na zamani, uwa uba kuma yadda masu hakar ma’adanai ba tare da izini ba suka mamaye bangaren. Wannan kuma yana samun bunkasa ne saboda yadda aka yi sakaci har ‘yan kasashe waje suka shigo suka mamaye bangaren suma suna hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba. Masana sun bayyana yadda hakar ma’adanai ba tare da cikakken izini ba ke cutar da muhalli da al’umma gaba daya.

ADVERTISEMENT

A ‘yan shekarun nan gwamnati ta dauki matakai na ganin an farfado da bangaren hakar ma’adanai, musamman ganin ana ganin lokaci ya yi da za a duba wasu bangarori don nema wa Nijeriya kudaden shiga saboda ganin yadda kasuwar albarkatun man fetur yake komawa baya.

Gwamnati ta dauki matakai masu muhimmanci don jawo hankalin ‘yan kasuwa da masu zuba jari na ciki da wajen kasa don su shigo a dama da su a harkar hakar ma’adanai a Nijeriya, kuma daga dukkan alamu wannan matakai sun fara haifar da da mai ido.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

Ga wanda yake son fadawa harkar hakar ma’adanai a Nijeriya ga wasu matakai masu muhimmanci da za su iya taimaka masa don gudanar da harkar kamar yadda doka ta tanada.

1). Samun Lasisi Daga Hukuma: kafin fara hakar ma’adanai yana da kyau mutum ya nemi izinin gwamnati ta hanyar samun lasisi na irin harka ma’adanan da zai yi. Laisisin da ake bayarwa sun hada da na masu dan karamin karfi da kuma na manya-manyan kamfanoni. Lasisin kuma zai iya kasancewa na mai haka kai staye ko mai sarrafawa, ko kuma na masu tsotso ruwa suna sayarwa, wato kamar masu ‘Fiya wata’ duk sai sun samu lasisi, ana kuma samun lasisin ne a karkashin ofishin gwmanati mai suna ‘Nigerian Cadastre’ wanda sune ke da alhakin sa ido a kan dukkan harkokin hakar ma’adanai a Nijeriya. A kwai kuma bukatar mutum ya nemi cikakken bayani na yadda ofishinsu ke aiki don ya samu saukin yin rajistar. Haka kuma cikin sharuddan dole mutum ya yi rajistar kamfaninsa tare da hukumar yi wa kamfanoni rajista a Nijeriya wato “Cooperate Affairs Commission” don sunan kamfanin mutum ya shiga cikin jerin kamfanoni da ke harkokinsu a Nijeriya, wannan na da matukar muhimmanci.
2). Bayanin Yadda Za A Gudanar Da Kasuwancin Ma’adanan ‘Business Plan’:
Akwai bukatar a samu cikakken bayani na irin ma’adanan da ake son fara haka da inda ake samunsu, yana kuma da muhimmanci a gudanar da bincike na kimiyya don sanin yawan ma’adanan a yankin, saboda ganin irin jarin da za a zuba.
3). Binciken Wurin Da Ake Son Gudanar Da Hakar Ma’adanan
Wannan kuma bincike ne na musamman da kwararru ke gudanarwa a wurin da ake son fara hakar ma’adanan don a gano hakikanin yawan ma’adanan da ke a cikin kasa, ta haka za a iya fahimtar yawa da ingancin ma’adanan don kada masu zuba jari su yi asara.
4). Binciken Kimiyya:
Binciken kimiyya a wurin da ake sa ran hakar ma’adanai yana bayar da bayanai don gane ainihin yawan ma’adanain da ake da shi a kasa da kuma yawan da za a iya hakowa a kullum. Wannan yana bayar da daman tsara yadda za a fuskanci aikin da yawan ma’akatan da ake bukata don samun cikakkiyar nasara.
5). Samar Da Kayyakin Aiki Na Zamani:
Yana da matukar muhimmanci samar da kayan aiki na zamani da za a gudanar da aiki a cikin sauki, wannan kuma ya hada da motoci na daukar ma’adanai da aka hako da muka ma’aikata.
6). Samar Da Wutar Lantarki Da Gidajen Ma’aikata
Yana da muhimmanci a samar da wurin kwana ga ma’aikata, yana kuma da kyau a gina gidan nesa da wurin da ake hakar ma’adanan saboda kariya daga cutar da ma’aikatan daga turirin ma’adanan da ake hakowa. Haka kuma samar da wutar lantarki na NEPA ko janaretab zai taimaka.
7). Fara Hakar Ma’adanan Gadan-gadan:
Daga nan kuma sai a fara aiki don ci gajiyar ma’adanan da aka shirya haka, ana taftacesu tare da wucewa da su kasuwa a ciki ko wajen kasa.

Yana kuma da muhimmanci a shigar da Sarakuna gargajiya da shugabanin matasa na yankin da ake hakar ma’adanan don kasancewa cikin jerin ma’aikata ko ‘yan kwangon da za su samar da wasu kayyakin aiki a ma’aikatar, wannan yana da matukar muhimmanci don rage kishi na ganin ana kwashe masu albarkatun kasa su kuma basu ci gajiyar abin ba. In har aka shigar da su, su da kansu za su ba harkar kariya daga duk wani abin da zai cutar da tafiyar saboda suma suna amfana. A na gaba za mu kawo muku irin ma’adanan da Allah ya shimfida a sassan Nijeriya.

Ma’adanai
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Next Post
BUA

Ta Ina Talakawa Za Su Mori Rage Farashin Simintin BUA?

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.