ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matakan Fara Sana’ar Hakar Ma’adanai Bisa Doka A Nijeriya

by Bello Hamza
3 years ago
Ma'adanai

Hakar ma’adanai na da matukar muhimmanci ga tattalin arzikin Nijeriya da ma Afirka gaba daya. Ta nan ne ake samar wa masana’antunmu na ciki da wajen kasa kayan sarrafawa, wanda kuma hakan ke samar da aikin yi ga dimbin matasa a ciki da wajen kasar nan.

A Nijeriya, tarihi ya nuna irin tasirin ma’adanai ga tattalin arzikin kasa inda ake samun fiye da kashi 0.3 na arzikin kasa daga bangaren ma’adanai (kamar yadda bayani ya nuna a kasafin kudin shekarar 2022). Bincike ya kuma nuna cewa, a yankin Afirka ake samun kashi 30 na dukkan ma’adanai na duniya, lamarin da ya sa Afirka a sahun gaba a harkar ma’adanai na duniya.

  • Matsalar Tsaro: Gwamnatin Zamfara Ta Haramta Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba
  • Kotun Sauraren Karar Zaben Gwamna A Legas Za Ta Yanke Hukunci Ranar Litinin

Duk da kasancewar harkar hakar ma’adanai na da muhimmanci ga tattalin arzikin Nijeriya amma har zuwa yanzu ba a kai ga bunkasa sashin ba yadda ya kamata, saboda rashin cikakken kayan aiki na zama da rashin masu zuba jari da kuma yadda har yanzu ake ci gaba da amfani kayan aikin hakar ma’adanai ba na zamani, uwa uba kuma yadda masu hakar ma’adanai ba tare da izini ba suka mamaye bangaren. Wannan kuma yana samun bunkasa ne saboda yadda aka yi sakaci har ‘yan kasashe waje suka shigo suka mamaye bangaren suma suna hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba. Masana sun bayyana yadda hakar ma’adanai ba tare da cikakken izini ba ke cutar da muhalli da al’umma gaba daya.

ADVERTISEMENT

A ‘yan shekarun nan gwamnati ta dauki matakai na ganin an farfado da bangaren hakar ma’adanai, musamman ganin ana ganin lokaci ya yi da za a duba wasu bangarori don nema wa Nijeriya kudaden shiga saboda ganin yadda kasuwar albarkatun man fetur yake komawa baya.

Gwamnati ta dauki matakai masu muhimmanci don jawo hankalin ‘yan kasuwa da masu zuba jari na ciki da wajen kasa don su shigo a dama da su a harkar hakar ma’adanai a Nijeriya, kuma daga dukkan alamu wannan matakai sun fara haifar da da mai ido.

LABARAI MASU NASABA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Ga wanda yake son fadawa harkar hakar ma’adanai a Nijeriya ga wasu matakai masu muhimmanci da za su iya taimaka masa don gudanar da harkar kamar yadda doka ta tanada.

1). Samun Lasisi Daga Hukuma: kafin fara hakar ma’adanai yana da kyau mutum ya nemi izinin gwamnati ta hanyar samun lasisi na irin harka ma’adanan da zai yi. Laisisin da ake bayarwa sun hada da na masu dan karamin karfi da kuma na manya-manyan kamfanoni. Lasisin kuma zai iya kasancewa na mai haka kai staye ko mai sarrafawa, ko kuma na masu tsotso ruwa suna sayarwa, wato kamar masu ‘Fiya wata’ duk sai sun samu lasisi, ana kuma samun lasisin ne a karkashin ofishin gwmanati mai suna ‘Nigerian Cadastre’ wanda sune ke da alhakin sa ido a kan dukkan harkokin hakar ma’adanai a Nijeriya. A kwai kuma bukatar mutum ya nemi cikakken bayani na yadda ofishinsu ke aiki don ya samu saukin yin rajistar. Haka kuma cikin sharuddan dole mutum ya yi rajistar kamfaninsa tare da hukumar yi wa kamfanoni rajista a Nijeriya wato “Cooperate Affairs Commission” don sunan kamfanin mutum ya shiga cikin jerin kamfanoni da ke harkokinsu a Nijeriya, wannan na da matukar muhimmanci.
2). Bayanin Yadda Za A Gudanar Da Kasuwancin Ma’adanan ‘Business Plan’:
Akwai bukatar a samu cikakken bayani na irin ma’adanan da ake son fara haka da inda ake samunsu, yana kuma da muhimmanci a gudanar da bincike na kimiyya don sanin yawan ma’adanan a yankin, saboda ganin irin jarin da za a zuba.
3). Binciken Wurin Da Ake Son Gudanar Da Hakar Ma’adanan
Wannan kuma bincike ne na musamman da kwararru ke gudanarwa a wurin da ake son fara hakar ma’adanan don a gano hakikanin yawan ma’adanan da ke a cikin kasa, ta haka za a iya fahimtar yawa da ingancin ma’adanan don kada masu zuba jari su yi asara.
4). Binciken Kimiyya:
Binciken kimiyya a wurin da ake sa ran hakar ma’adanai yana bayar da bayanai don gane ainihin yawan ma’adanain da ake da shi a kasa da kuma yawan da za a iya hakowa a kullum. Wannan yana bayar da daman tsara yadda za a fuskanci aikin da yawan ma’akatan da ake bukata don samun cikakkiyar nasara.
5). Samar Da Kayyakin Aiki Na Zamani:
Yana da matukar muhimmanci samar da kayan aiki na zamani da za a gudanar da aiki a cikin sauki, wannan kuma ya hada da motoci na daukar ma’adanai da aka hako da muka ma’aikata.
6). Samar Da Wutar Lantarki Da Gidajen Ma’aikata
Yana da muhimmanci a samar da wurin kwana ga ma’aikata, yana kuma da kyau a gina gidan nesa da wurin da ake hakar ma’adanan saboda kariya daga cutar da ma’aikatan daga turirin ma’adanan da ake hakowa. Haka kuma samar da wutar lantarki na NEPA ko janaretab zai taimaka.
7). Fara Hakar Ma’adanan Gadan-gadan:
Daga nan kuma sai a fara aiki don ci gajiyar ma’adanan da aka shirya haka, ana taftacesu tare da wucewa da su kasuwa a ciki ko wajen kasa.

Yana kuma da muhimmanci a shigar da Sarakuna gargajiya da shugabanin matasa na yankin da ake hakar ma’adanan don kasancewa cikin jerin ma’aikata ko ‘yan kwangon da za su samar da wasu kayyakin aiki a ma’aikatar, wannan yana da matukar muhimmanci don rage kishi na ganin ana kwashe masu albarkatun kasa su kuma basu ci gajiyar abin ba. In har aka shigar da su, su da kansu za su ba harkar kariya daga duk wani abin da zai cutar da tafiyar saboda suma suna amfana. A na gaba za mu kawo muku irin ma’adanan da Allah ya shimfida a sassan Nijeriya.

Ma’adanai
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja

MASU ALAKA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
BUA

Ta Ina Talakawa Za Su Mori Rage Farashin Simintin BUA?

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.