• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikita-rikitar Da Ta Biyo Bayan Mutuwar Mawaki Mohbad

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Nishadi
0
Rikita-rikitar Da Ta Biyo Bayan Mutuwar Mawaki Mohbad
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mutuwar shahararren mawaki Ilerioluwa Aloba, wanda aka fi sani da Mohbad it ace maganar da aka shafe kusan makonni biyu ana tattauna ta a shafukan sada zumunta a fadin kasar nan baki daya.

Mawakin mai shekaru 27 ya rasu ne a ranar 12 ga watan Satumba cikin wani yanayi mai cike da rudani da ya janyo ce-ce-ku-ce a tsakanin abokan sana’ar sa a jihar Legas.

  • A Shirye Sin Take Ta Inganta Hadin Gwiwa Da UNESCO Domin Samar Da Ci Gaba Da Zaman Lafiya A Duniya
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Asirce: Sa-in-sa Ta Kaure Tsakanin Gwamnatin Tarayya Da Ta Zamfara

Sai dai wani abu mai kama da zargi da rudani shi ne kwana daya bayan rasuwarsa aka yi jana’izarsa, wani abu da shi ma ya janyo ka-ce-na-ce saboda abune wanda ba’a saba gani ba kasancewar sa ba musilmi ba ne kuma akanyi bukuku musamman idan wani ya mutu a cikin kabilar da aka haife shi.

Amma kuma a ranar Alhamis ‘yan sanda suka tono gawar Mohbad domin gudanar da bincike bayan da aka yi ta samun korafe-korafe har daga mawaka abokansa.

Itama gwamnatin jihar Legas karkashin mulkin Babajide Sanwo-Olu, ta bayar  da umurni a hukunta duk wanda ya taka wata rawa da ta kai ga mutuwar mawakin.

Labarai Masu Nasaba

Ya Kamata Mata ‘Yan Fim Su Rike Mutuncin Kansu – Aisha Tafida Gombe

Saboda In Nuna Wa Duniya Asalin Al’adar Bahaushe Ya Sa Na Fara Fina-finan Turanci A Arewacin Nijeriya – Jammaje

Ya yinda rundunar  ‘yan sandan jihar Legas  ta ce ta kammala bincike kan gawar mawaki Ilerioluwa Aloba, wanda aka fi sani da Mohbad kuma a cewar rundunar, ta kammala binciken cikin nasara.

Dubban mutane ne suka yi zanga-zanga a sassan kasar nan musamman ma dai a jihar Legas da makwabtan jihohi domin nuna fushinsu kan yadda mawakin na Afrobeat ya mutu cikin wani yanayi mai cike da alamar tambaya.

A birnin Legas, an yi wani taro na zaman jimami a ranar Alhamis din satin da ya gabata inda aka ga matasa suna tattaki suna kiran da a bi wa mawakin kadinsa.

Rahotanni sun ce fitattun mawaka irinsu Dabido, Zlatan da Falz sun halarci taron zaman jimamin duk da cewa hukumomi sun gudanar da bincike kan gawar Mohbad.

Mohbad ya rasu ne bayan da aka garzaya da shi wani asibiti bisa wani rashin lafiya da ba a sani ba sai dai bayanai sun yi nuni da cewa, an yi wa mawakin wata allura a lokacin da aka kai shi asibitin inda daga nan kuma sai rai ya yi halinsa.

Mohbad, wanda a da mawaki ne karkashin kamfanin Malians na fitccen mawaki Naira Marley, ya fito idon duniya da wakokinsa irinsu ‘Ponmo, Peace, Ask About Me’ da sauransu.

A bara ne ya kuma fice daga kamfanin bisa wasu dalilai da har yanzu ba a fayyace ba sai dai daman hakan baya rasa nasaba da irin rikice-rikice da ake yawan samu a tsakanin masu irin wannan sana’ar Itama kungiyar nan ta kare muradun yarabawa da OPC ta bukaci gwamnati da jami’an tsaro akan suyi iya yinsu domin ganin an yiwa marigayi Mohbad adalci.

Kungiyar tace da ace marigayi Mohbad ya bayyana halin firgici da tashin hankalin da yake ciki ga kungiyar da tuni ba a kai ga haka ba kuma za su dauki matakin kare shi daga masu yi masa barazana ga rayuwa.

Kungiyar OPC dai ta bukaci rundunar ‘yan sanda ta kasa da jami’an hukumar tsaro ta farin kaya DSS da suyi kokarin gano wadanda suka kashe mawakin domin a hukunta su.

Wani tsohon faifan bidiyo na Bella Shmurda yana cewa Mohbad yana fama da matsalar tabin hankali kwanan nan ya sake kunno kai a yanar gizo mintuna bayan mutuwar mawakin.

Bayanai kan musabbabin mutuwarsa da kuma inda ya rasu yana ci gaba da zayyana har lokacin da ake hada wannan rahoto.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaba Xi Ya Jinjinawa Jaruman Kasar Da Suka Kwanta Dama A Ranar Shahidan Kasar Sin

Next Post

AU Ta Yi Kira Da Kara Zurfafa Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Afirka Da Sin

Related

Ya Kamata Mata ‘Yan Fim Su Rike Mutuncin Kansu – Aisha Tafida Gombe
Nishadi

Ya Kamata Mata ‘Yan Fim Su Rike Mutuncin Kansu – Aisha Tafida Gombe

5 days ago
Saboda In Nuna Wa Duniya Asalin Al’adar Bahaushe Ya Sa Na Fara Fina-finan Turanci A Arewacin Nijeriya – Jammaje
Nishadi

Saboda In Nuna Wa Duniya Asalin Al’adar Bahaushe Ya Sa Na Fara Fina-finan Turanci A Arewacin Nijeriya – Jammaje

2 weeks ago
Daga Kaina An Gama Harkar Fim A Zuri’ata – Moda
Nishadi

Daga Kaina An Gama Harkar Fim A Zuri’ata – Moda

2 weeks ago
Rarara Zai Angwance Da Aisha Humaira Yau A Maiduguri
Manyan Labarai

Rarara Zai Angwance Da Aisha Humaira Yau A Maiduguri

2 weeks ago
Jerin Manyan Jaruman Fim Da Nijeriya Ta Rasa A Yan Shekarun Nan
Nishadi

Jerin Manyan Jaruman Fim Da Nijeriya Ta Rasa A Yan Shekarun Nan

3 weeks ago
Me Ya Janyo Jifan Mawaka A Arewacin Nijeriya?
Nishadi

Me Ya Janyo Jifan Mawaka A Arewacin Nijeriya?

4 weeks ago
Next Post
AU Ta Yi Kira Da Kara Zurfafa Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Afirka Da Sin

AU Ta Yi Kira Da Kara Zurfafa Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Afirka Da Sin

LABARAI MASU NASABA

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta ÆŠage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta ÆŠage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.