ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Asirce: Sa-in-sa Ta Kaure Tsakanin Gwamnatin Tarayya Da Ta Zamfara

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Bindiga

LABARAI MASU NASABA

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Gwamnatin tarayya ta caccaki gwamnatin Jihar Zamfara bisa zargin da ake yi na sanya siyasa a sace daliban jami’ar tarayya ta Gusau (FUGUS) a jihar.

Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a na kasa, Alhaji Mohammed Idris, shi ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Abuja ranar Litinin da ta gabata, ya nuna rashin jin dadinsa ga kalaman gwamnan Jihar Zamfara, Dakta Dauda Lawal, maimakon yaba wa jami’an tsaro da kuma hukumomin gwamnatin tarayya don gaggawar kokarin kubutar da daliban da aka sace, sai gwamnatin Zamfara ta saka siyasa cikin lamarin domin cimma birinta na siyasa.

  • CMG Ta Kaddamar Da Wani Biki Don Fara Nuna Shirin “Journey Through Civilizations” A Kasar Peru
  • NLC Da TUC Sun Shirya Tsunduma Yajin Aiki Mai Dogon Zango Ranar Talata 3 Ga Oktoba 2023

Ministan ya ce doka ta ba wa hukumomin gwamnatin tarayya ikon daukar mataki ba tare da wani dalili ba, domin tabbatar da tsaron rayukan ‘yan kasar da aka yi garkuwa da su, kamar yadda aka yi ga wadannan daliban.

Ya ce kasancewar hukumomin da ke da alhakkin ba su cikakken bayani kan irin wadannan ayyuka, hakan bai zama na sirri ba, kamar yadda gwamnatin Jihar Zamfara ta bayyana munin lamarin.

Ministan ya bayyana cewa domin kauce wa shakku, babu wani jami’in gwamnatin tarayya da ke tattaunawa da wani dan fashin daji ko kungiyar ‘yan bindiga.

Ya ce duk da haka gwamnati tana ci gaba da yunkurin gano duk wata hanyar da za ta iya haifar da tashin hankali tare da dawo da zaman lafiya a cikin al’ummomin da ‘yan fashi suka tarwatsa.

Ya ce idan al’ummomi suka yanke shawarar neman taimaka wajen kawo karshen tashe-tashen hankula a wasu sassan kasar nan domin su shiga tattaunawa, gwamnatin tarayya ba za ta yi gaggawar yin Allah wadai da irin wannan yunkuri na mutane ba.

Ministan ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa gwamnatin tarayya da hukumominta suna bakin kokarinsu wajen ganin an kawo karshen matsalar ‘yan bindiga masu garkuwa da mutane da duk wani nau’i na aikata mummunan laifuka.

Ya ce bambance-bambancen siyasa ko fada a tsakanin juna bai kamata a shigo da shi cikin wani muhimmin al’amari da ya shafi tsaron kasa ba, domin kauce wa ruguza kokarin sojojin ko kuma kawo cikas ga kokarin gwamnatin tarayya.

Ministan ya ce gwamnatin tarayya a shirye take ta saurara tare da ci gaba da haad kai da duk masu ruwa da tsaki a fadin kasar nan wajen samar da mafita mai dorewa ga matsalolin tsaro.

“Muna kira ga kowa da kowa da a hada hannu da mu domin samun mafita,” in ji minista.

Sai dai a bangare daya kuma, Gwamna Lawal, ya ce Gwamnatin Zamfara tana da gamsassun hujjoji da ke fallasa wasu jami’an Gwamnatin Tarayya da hannu a shirya zaman sulhu da ‘yan bindiga.

A wata takardar da aka rabawa manema labarai, mai magana da yawun gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya bayyana cewa gwamnatin Dauda Lawal tana da hujjoji masu tada hankali da ke fallasa wasu jami’an Gwamnatin Tarayya kan sulhu da ‘yan bindiga.

Ya kara da cewa ministan labarai ya yi ri-ga mallam masallaci wurin yanke hukunci tare da yanke wa gwamnatin Zamfara hanzari.

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Mun nemi karin bayani daga Gwamnatin Tarayya kan zaman sirri na sulhu da wasu jami’anta suke jagoranta a Zamfara ba tare da sanin gwamnatin jiha ko shugabanni jami’an tsaron jihar ba.

“Muna da gamsassun hujjoji da ke tabbatar da wannan zaman sulhu tsakanin jami’an Gwamnatin Tarayya da ‘yan bindiga a wurare mabambanta a Zamfara.

“Akwai ban takaici a ce ministan yada labarai zai fito bainar jama’a ya kore batun ba tare da ya nemi sani daga jami’an tsaro ko ‘yan uwanshi da ke da hannu dumu-dumu a lamarin ba. Mun tsammaci tun da kwararre ne a harka watsa labarai zai bi matakan da ilimi ya shardanta don tabbatarwa ko kore batun namu.

“Gwamnatin Jihar Zamfara tana matukar mutunta ka’ida tare da ganin kimar hukuma. Ba za mu fito kafafen watsa labarai muna fallasa sunayen jami’an Gwamnatin Tarayyan da ke wannan ta’asa ba, amma mun sanar da ‘yan Nijeriya don su nemi karin bayani daga Gwamnatin Tarayya.

“Muna so mu sanar da minista cewa jami’ansu na Gwamnatin Tarayya da ke jagorantar wannan zaman sulhu da ‘yan bindiga su ne ke siyasantar da matsalar tsaro ba Gwamnatin Zamfara ba.

“Ba mu san daga inda ministan ya samu kwarin gwiwan bugun kirji ya ce babu wani zaman sulhu da aka yi a Zamfara ba, saboda ai mun bayyana wuraren da aka yi wadannan zama, irinsu Birnin Magaji, Maradun, Mun Haye, Ajah, Bawo, da kuma Bagege.

“Muna sake nanatawa cewa sulhu da ‘yan bindiga a Zamfara ba zai taba haifar da da mai ido ba. Sam! Ba wannan ba ne mafita ga matsalar, a yi amfani da karfi kawai a kauda su, wanna ita ce matsayarmu har gobe.

“Muna kira ga Gwamnatin Tarayya da ta daina biye wa ‘yan amshin Shata, ta yi bincike tare da wanke kanta daga aikin wadannan dillalan sulhu da ‘yan bindiga.”

Shi ma ministan tsaro, Mohammed Badaru Abubakar, ya musanta zargin cewa gwamnatin tarayya na tattaunawa da ‘yan bindiga a Jihar Zamfara a asirce ba tare da sanin gwamnatin jihar ba.

Ministan ya bayyana haka ne a yayin da yake mayar da martani a wata takarda da ya aike wa Gwamna Dauda Lawal wanda ya yi zargin cewa, gwamnatin tarayya na tattaunawa da ‘yan ta’addan Zamfara domin ganin an sako mutanen da aka sace.

Ministan ya yi watsi da zargin, yana mai nuni da cewa “Gwamnatin Tarayya tana aiki ba dare ba rana domin ganin an ceto ‘yan matan jami’an tarayya ta Gusau da sauran wadanda aka sace sun sake hadewa da iyalansu.

Ministan a cikin wata sanarwa da mukaddashin daraktan hulda da jama’a na ma’aikatar tsaro (MOD), Attari Hope, ya fitar a ranar Litinin, ya bayyana kwarin gwiwar cewa, jami’an tsaro na hadin gwiwa da ke aiki ba dare ba rana za su ceto daliban.

Ministan ya ce, “Zargin karya ne kuma yaudara ce domin ma’aikatar tsaro ba ta umurci wani ko wata kungiya da su tattauna a madadin gwamnatin tarayya ba.”

Bindiga
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
Yadda Miliyoyin Yaran Nijeriya Ke Fama Da Aikatau

Yadda Miliyoyin Yaran Nijeriya Ke Fama Da Aikatau

LABARAI MASU NASABA

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.