ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Asirce: Sa-in-sa Ta Kaure Tsakanin Gwamnatin Tarayya Da Ta Zamfara

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Bindiga

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Gwamnatin tarayya ta caccaki gwamnatin Jihar Zamfara bisa zargin da ake yi na sanya siyasa a sace daliban jami’ar tarayya ta Gusau (FUGUS) a jihar.

Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a na kasa, Alhaji Mohammed Idris, shi ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Abuja ranar Litinin da ta gabata, ya nuna rashin jin dadinsa ga kalaman gwamnan Jihar Zamfara, Dakta Dauda Lawal, maimakon yaba wa jami’an tsaro da kuma hukumomin gwamnatin tarayya don gaggawar kokarin kubutar da daliban da aka sace, sai gwamnatin Zamfara ta saka siyasa cikin lamarin domin cimma birinta na siyasa.

  • CMG Ta Kaddamar Da Wani Biki Don Fara Nuna Shirin “Journey Through Civilizations” A Kasar Peru
  • NLC Da TUC Sun Shirya Tsunduma Yajin Aiki Mai Dogon Zango Ranar Talata 3 Ga Oktoba 2023

Ministan ya ce doka ta ba wa hukumomin gwamnatin tarayya ikon daukar mataki ba tare da wani dalili ba, domin tabbatar da tsaron rayukan ‘yan kasar da aka yi garkuwa da su, kamar yadda aka yi ga wadannan daliban.

Ya ce kasancewar hukumomin da ke da alhakkin ba su cikakken bayani kan irin wadannan ayyuka, hakan bai zama na sirri ba, kamar yadda gwamnatin Jihar Zamfara ta bayyana munin lamarin.

Ministan ya bayyana cewa domin kauce wa shakku, babu wani jami’in gwamnatin tarayya da ke tattaunawa da wani dan fashin daji ko kungiyar ‘yan bindiga.

Ya ce duk da haka gwamnati tana ci gaba da yunkurin gano duk wata hanyar da za ta iya haifar da tashin hankali tare da dawo da zaman lafiya a cikin al’ummomin da ‘yan fashi suka tarwatsa.

Ya ce idan al’ummomi suka yanke shawarar neman taimaka wajen kawo karshen tashe-tashen hankula a wasu sassan kasar nan domin su shiga tattaunawa, gwamnatin tarayya ba za ta yi gaggawar yin Allah wadai da irin wannan yunkuri na mutane ba.

Ministan ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa gwamnatin tarayya da hukumominta suna bakin kokarinsu wajen ganin an kawo karshen matsalar ‘yan bindiga masu garkuwa da mutane da duk wani nau’i na aikata mummunan laifuka.

Ya ce bambance-bambancen siyasa ko fada a tsakanin juna bai kamata a shigo da shi cikin wani muhimmin al’amari da ya shafi tsaron kasa ba, domin kauce wa ruguza kokarin sojojin ko kuma kawo cikas ga kokarin gwamnatin tarayya.

Ministan ya ce gwamnatin tarayya a shirye take ta saurara tare da ci gaba da haad kai da duk masu ruwa da tsaki a fadin kasar nan wajen samar da mafita mai dorewa ga matsalolin tsaro.

“Muna kira ga kowa da kowa da a hada hannu da mu domin samun mafita,” in ji minista.

Sai dai a bangare daya kuma, Gwamna Lawal, ya ce Gwamnatin Zamfara tana da gamsassun hujjoji da ke fallasa wasu jami’an Gwamnatin Tarayya da hannu a shirya zaman sulhu da ‘yan bindiga.

A wata takardar da aka rabawa manema labarai, mai magana da yawun gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya bayyana cewa gwamnatin Dauda Lawal tana da hujjoji masu tada hankali da ke fallasa wasu jami’an Gwamnatin Tarayya kan sulhu da ‘yan bindiga.

Ya kara da cewa ministan labarai ya yi ri-ga mallam masallaci wurin yanke hukunci tare da yanke wa gwamnatin Zamfara hanzari.

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Mun nemi karin bayani daga Gwamnatin Tarayya kan zaman sirri na sulhu da wasu jami’anta suke jagoranta a Zamfara ba tare da sanin gwamnatin jiha ko shugabanni jami’an tsaron jihar ba.

“Muna da gamsassun hujjoji da ke tabbatar da wannan zaman sulhu tsakanin jami’an Gwamnatin Tarayya da ‘yan bindiga a wurare mabambanta a Zamfara.

“Akwai ban takaici a ce ministan yada labarai zai fito bainar jama’a ya kore batun ba tare da ya nemi sani daga jami’an tsaro ko ‘yan uwanshi da ke da hannu dumu-dumu a lamarin ba. Mun tsammaci tun da kwararre ne a harka watsa labarai zai bi matakan da ilimi ya shardanta don tabbatarwa ko kore batun namu.

“Gwamnatin Jihar Zamfara tana matukar mutunta ka’ida tare da ganin kimar hukuma. Ba za mu fito kafafen watsa labarai muna fallasa sunayen jami’an Gwamnatin Tarayyan da ke wannan ta’asa ba, amma mun sanar da ‘yan Nijeriya don su nemi karin bayani daga Gwamnatin Tarayya.

“Muna so mu sanar da minista cewa jami’ansu na Gwamnatin Tarayya da ke jagorantar wannan zaman sulhu da ‘yan bindiga su ne ke siyasantar da matsalar tsaro ba Gwamnatin Zamfara ba.

“Ba mu san daga inda ministan ya samu kwarin gwiwan bugun kirji ya ce babu wani zaman sulhu da aka yi a Zamfara ba, saboda ai mun bayyana wuraren da aka yi wadannan zama, irinsu Birnin Magaji, Maradun, Mun Haye, Ajah, Bawo, da kuma Bagege.

“Muna sake nanatawa cewa sulhu da ‘yan bindiga a Zamfara ba zai taba haifar da da mai ido ba. Sam! Ba wannan ba ne mafita ga matsalar, a yi amfani da karfi kawai a kauda su, wanna ita ce matsayarmu har gobe.

“Muna kira ga Gwamnatin Tarayya da ta daina biye wa ‘yan amshin Shata, ta yi bincike tare da wanke kanta daga aikin wadannan dillalan sulhu da ‘yan bindiga.”

Shi ma ministan tsaro, Mohammed Badaru Abubakar, ya musanta zargin cewa gwamnatin tarayya na tattaunawa da ‘yan bindiga a Jihar Zamfara a asirce ba tare da sanin gwamnatin jihar ba.

Ministan ya bayyana haka ne a yayin da yake mayar da martani a wata takarda da ya aike wa Gwamna Dauda Lawal wanda ya yi zargin cewa, gwamnatin tarayya na tattaunawa da ‘yan ta’addan Zamfara domin ganin an sako mutanen da aka sace.

Ministan ya yi watsi da zargin, yana mai nuni da cewa “Gwamnatin Tarayya tana aiki ba dare ba rana domin ganin an ceto ‘yan matan jami’an tarayya ta Gusau da sauran wadanda aka sace sun sake hadewa da iyalansu.

Ministan a cikin wata sanarwa da mukaddashin daraktan hulda da jama’a na ma’aikatar tsaro (MOD), Attari Hope, ya fitar a ranar Litinin, ya bayyana kwarin gwiwar cewa, jami’an tsaro na hadin gwiwa da ke aiki ba dare ba rana za su ceto daliban.

Ministan ya ce, “Zargin karya ne kuma yaudara ce domin ma’aikatar tsaro ba ta umurci wani ko wata kungiya da su tattauna a madadin gwamnatin tarayya ba.”

Bindiga
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Next Post
Yadda Miliyoyin Yaran Nijeriya Ke Fama Da Aikatau

Yadda Miliyoyin Yaran Nijeriya Ke Fama Da Aikatau

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.