ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikita-rikitar Da Ta Biyo Bayan Mutuwar Mawaki Mohbad

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Mohbad

Mutuwar shahararren mawaki Ilerioluwa Aloba, wanda aka fi sani da Mohbad it ace maganar da aka shafe kusan makonni biyu ana tattauna ta a shafukan sada zumunta a fadin kasar nan baki daya.

Mawakin mai shekaru 27 ya rasu ne a ranar 12 ga watan Satumba cikin wani yanayi mai cike da rudani da ya janyo ce-ce-ku-ce a tsakanin abokan sana’ar sa a jihar Legas.

  • A Shirye Sin Take Ta Inganta Hadin Gwiwa Da UNESCO Domin Samar Da Ci Gaba Da Zaman Lafiya A Duniya
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Asirce: Sa-in-sa Ta Kaure Tsakanin Gwamnatin Tarayya Da Ta Zamfara

Sai dai wani abu mai kama da zargi da rudani shi ne kwana daya bayan rasuwarsa aka yi jana’izarsa, wani abu da shi ma ya janyo ka-ce-na-ce saboda abune wanda ba’a saba gani ba kasancewar sa ba musilmi ba ne kuma akanyi bukuku musamman idan wani ya mutu a cikin kabilar da aka haife shi.

ADVERTISEMENT

Amma kuma a ranar Alhamis ‘yan sanda suka tono gawar Mohbad domin gudanar da bincike bayan da aka yi ta samun korafe-korafe har daga mawaka abokansa.

Itama gwamnatin jihar Legas karkashin mulkin Babajide Sanwo-Olu, ta bayar  da umurni a hukunta duk wanda ya taka wata rawa da ta kai ga mutuwar mawakin.

LABARAI MASU NASABA

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

Ya yinda rundunar  ‘yan sandan jihar Legas  ta ce ta kammala bincike kan gawar mawaki Ilerioluwa Aloba, wanda aka fi sani da Mohbad kuma a cewar rundunar, ta kammala binciken cikin nasara.

Dubban mutane ne suka yi zanga-zanga a sassan kasar nan musamman ma dai a jihar Legas da makwabtan jihohi domin nuna fushinsu kan yadda mawakin na Afrobeat ya mutu cikin wani yanayi mai cike da alamar tambaya.

A birnin Legas, an yi wani taro na zaman jimami a ranar Alhamis din satin da ya gabata inda aka ga matasa suna tattaki suna kiran da a bi wa mawakin kadinsa.

Rahotanni sun ce fitattun mawaka irinsu Dabido, Zlatan da Falz sun halarci taron zaman jimamin duk da cewa hukumomi sun gudanar da bincike kan gawar Mohbad.

Mohbad ya rasu ne bayan da aka garzaya da shi wani asibiti bisa wani rashin lafiya da ba a sani ba sai dai bayanai sun yi nuni da cewa, an yi wa mawakin wata allura a lokacin da aka kai shi asibitin inda daga nan kuma sai rai ya yi halinsa.

Mohbad, wanda a da mawaki ne karkashin kamfanin Malians na fitccen mawaki Naira Marley, ya fito idon duniya da wakokinsa irinsu ‘Ponmo, Peace, Ask About Me’ da sauransu.

A bara ne ya kuma fice daga kamfanin bisa wasu dalilai da har yanzu ba a fayyace ba sai dai daman hakan baya rasa nasaba da irin rikice-rikice da ake yawan samu a tsakanin masu irin wannan sana’ar Itama kungiyar nan ta kare muradun yarabawa da OPC ta bukaci gwamnati da jami’an tsaro akan suyi iya yinsu domin ganin an yiwa marigayi Mohbad adalci.

Kungiyar tace da ace marigayi Mohbad ya bayyana halin firgici da tashin hankalin da yake ciki ga kungiyar da tuni ba a kai ga haka ba kuma za su dauki matakin kare shi daga masu yi masa barazana ga rayuwa.

Kungiyar OPC dai ta bukaci rundunar ‘yan sanda ta kasa da jami’an hukumar tsaro ta farin kaya DSS da suyi kokarin gano wadanda suka kashe mawakin domin a hukunta su.

Wani tsohon faifan bidiyo na Bella Shmurda yana cewa Mohbad yana fama da matsalar tabin hankali kwanan nan ya sake kunno kai a yanar gizo mintuna bayan mutuwar mawakin.

Bayanai kan musabbabin mutuwarsa da kuma inda ya rasu yana ci gaba da zayyana har lokacin da ake hada wannan rahoto.

Mohbad
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Yaushe Za A Fara Kofin Zakarun Turai
  • Abba Ibrahim Wada
    Messi Ya Yi Ritaya A Argentina: Da Me Za Mu Iya Tuna Gwarzon Duniyar?
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye ‘Yan wasan Nijeriya Da Za Su Buga Gasar Firimiyar Ingila Ta Bana?
  • Abba Ibrahim Wada
    Chelsea A Ƙarƙashin Xavi Alonso

MASU ALAKA

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
Nishadi

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

September 5, 2026
Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood
Nishadi

Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

August 29, 2026
Mohbad
Nishadi

Dalilan Da Suka Sa Ba Zan Iya Auren Ɗan Film Ba —Bilkisu Bishasha

August 23, 2026
Next Post
AU Ta Yi Kira Da Kara Zurfafa Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Afirka Da Sin

AU Ta Yi Kira Da Kara Zurfafa Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Afirka Da Sin

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.