• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Danbarwar Auren Sadiya Haruna Da G-Fresh Ta Dawo

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Nishadi
0
Danbarwar Auren Sadiya Haruna Da G-Fresh Ta Dawo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kotun  sharia’r musulunci dake zamanta a filin hoki dake Kano ta  umarci mai barkwancin nan na manhajar TikTok, Abubakar Ibrahim da aka fi sani da  G-Fresh da ya koma yayi bikon matarsa, sayyada Sadiya Haruna, wadda aka ruwaito cewa tayi yaji.

Kamar yadda kotun ta bayyana, tunda G Fresh bai saki matarsa ba akwai bukatar yayi bikon ta domin ci gaba da zaman aure kamar yadda addinin musulunci ya tsara ga duk wadda tayi yaji.

  • Kotu Ta Kori Kakakin Majalisar Dokokin Filato
  • Yadda Alakar Sin Da Afirka Ke Kara Bunkasa Kasashen Nahiyar Afirka

Lauya mai kare G Fresh Barr. Fatima Aliyu ta bayyana cewar har yanzu G Fresh na matukar kaunar matar sa wanda hakan yasa ba zai iya rabuwa da ita ba kuma shima G-Fresh din yasha nanatawa a shafinsa na TikTok cewa yana son matarsa kuma ba zai iya rabuwa da ita ba.

Kotun dai ta bayar da daga yau zuwa ranar 10 ga watan Oktoba mai kamawa domin G Fresh ya sulhunta da matarsa Sayyada Sadiya Haruna kuma ta koma su ci gaba da zaman auren su.

A kwanakin baya ne dai aka dinga yada wata jita-jita cewar auren taurarin Tiktok din, Sayyada Sadiya Haruna da G-Fresh Al-Ameen  Kano state material ya mutu, sai dai daga baya ya fito ya bayyana cewa auren yana nan daram ba kamar yadda ake ta yayatawa ba.

Labarai Masu Nasaba

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

A ranar 16 ga Yunin da ya wuce ne aka daura auren shahararrun masoyan na TikTok, auren da ya dauki hankulan mutane da dama musamman masu amfani da kafofin sada zumunta na zamani da suka hada da Facebook da D da kuma TikTok din.

Sai dai Jim kadan bayan tarewar Ango a gidan Amarya kuma sai ta tafi aikin Hajji a kasa mai tsarki wanda hakan tasa G-Fresh kullum ya dinga yada bidiyon sa, yana sambatun shaukin rabuwa da amaryarsa.

Amma bayan dawowar amarya sai ga labari ya cika TikTok da sauran kafafen sada zumunta cewa wai auren taurarin biyu ya mutu inda har ma wasu ‘yan TikTok na cewa wai G-fresh ya yi yaji ne daga gidan Sayyada Sadiya ya koma kwanan shago bayan da aka samu sabani a tsakaninsu.

Amma daga baya kuma aka gano cewa har yanzu Al-ameen G-fresh Kano state material ya na nan a dakin matarsa Sayyada Sadiya Haruna kuma shima ya nanata hakan.

Wasu rahotanni sun ruwaito cewar tun farko Sayyada Sadiya ta mayar da shafinta na TikTok wurin tallata magunagunan gargajiya da take sayarwa kuma ta goge duk wani bidiyo da ta yi a baya ciki kuwa har da bidiyoyin soyayyarsu da Kano state material din.

Sai dai goge bidiyon ne yasa wasu  suka fara yada jita-jitar cewa an samu matsala tsakanin ma’auratan guda biyu wadanda soyayyar su ya karade ko ina a shafukan sada zumunta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Jaddada Aniyar Magance Rashin Tsaro Da Talauci A Nijeriya

Next Post

Za A Wallafa Sharhin Xi Kan Ciyar Da Zamanantar Da Kasar Sin Gaba

Related

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan
Nishadi

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

2 days ago
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango
Nishadi

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

3 days ago
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)
Nishadi

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

1 week ago
Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba
Nishadi

Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba

2 weeks ago
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah
Nishadi

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

3 weeks ago
Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya
Nishadi

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

1 month ago
Next Post
Za A Wallafa Sharhin Xi Kan Ciyar Da Zamanantar Da Kasar Sin Gaba

Za A Wallafa Sharhin Xi Kan Ciyar Da Zamanantar Da Kasar Sin Gaba

LABARAI MASU NASABA

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

September 16, 2025
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

September 16, 2025
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

September 16, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

September 16, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan DimokuraÉ—iyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan DimokuraÉ—iyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.