• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Danbarwar Auren Sadiya Haruna Da G-Fresh Ta Dawo

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Nishadi
0
Danbarwar Auren Sadiya Haruna Da G-Fresh Ta Dawo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kotun  sharia’r musulunci dake zamanta a filin hoki dake Kano ta  umarci mai barkwancin nan na manhajar TikTok, Abubakar Ibrahim da aka fi sani da  G-Fresh da ya koma yayi bikon matarsa, sayyada Sadiya Haruna, wadda aka ruwaito cewa tayi yaji.

Kamar yadda kotun ta bayyana, tunda G Fresh bai saki matarsa ba akwai bukatar yayi bikon ta domin ci gaba da zaman aure kamar yadda addinin musulunci ya tsara ga duk wadda tayi yaji.

  • Kotu Ta Kori Kakakin Majalisar Dokokin Filato
  • Yadda Alakar Sin Da Afirka Ke Kara Bunkasa Kasashen Nahiyar Afirka

Lauya mai kare G Fresh Barr. Fatima Aliyu ta bayyana cewar har yanzu G Fresh na matukar kaunar matar sa wanda hakan yasa ba zai iya rabuwa da ita ba kuma shima G-Fresh din yasha nanatawa a shafinsa na TikTok cewa yana son matarsa kuma ba zai iya rabuwa da ita ba.

Kotun dai ta bayar da daga yau zuwa ranar 10 ga watan Oktoba mai kamawa domin G Fresh ya sulhunta da matarsa Sayyada Sadiya Haruna kuma ta koma su ci gaba da zaman auren su.

A kwanakin baya ne dai aka dinga yada wata jita-jita cewar auren taurarin Tiktok din, Sayyada Sadiya Haruna da G-Fresh Al-Ameen  Kano state material ya mutu, sai dai daga baya ya fito ya bayyana cewa auren yana nan daram ba kamar yadda ake ta yayatawa ba.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

A ranar 16 ga Yunin da ya wuce ne aka daura auren shahararrun masoyan na TikTok, auren da ya dauki hankulan mutane da dama musamman masu amfani da kafofin sada zumunta na zamani da suka hada da Facebook da D da kuma TikTok din.

Sai dai Jim kadan bayan tarewar Ango a gidan Amarya kuma sai ta tafi aikin Hajji a kasa mai tsarki wanda hakan tasa G-Fresh kullum ya dinga yada bidiyon sa, yana sambatun shaukin rabuwa da amaryarsa.

Amma bayan dawowar amarya sai ga labari ya cika TikTok da sauran kafafen sada zumunta cewa wai auren taurarin biyu ya mutu inda har ma wasu ‘yan TikTok na cewa wai G-fresh ya yi yaji ne daga gidan Sayyada Sadiya ya koma kwanan shago bayan da aka samu sabani a tsakaninsu.

Amma daga baya kuma aka gano cewa har yanzu Al-ameen G-fresh Kano state material ya na nan a dakin matarsa Sayyada Sadiya Haruna kuma shima ya nanata hakan.

Wasu rahotanni sun ruwaito cewar tun farko Sayyada Sadiya ta mayar da shafinta na TikTok wurin tallata magunagunan gargajiya da take sayarwa kuma ta goge duk wani bidiyo da ta yi a baya ciki kuwa har da bidiyoyin soyayyarsu da Kano state material din.

Sai dai goge bidiyon ne yasa wasu  suka fara yada jita-jitar cewa an samu matsala tsakanin ma’auratan guda biyu wadanda soyayyar su ya karade ko ina a shafukan sada zumunta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Jaddada Aniyar Magance Rashin Tsaro Da Talauci A Nijeriya

Next Post

Za A Wallafa Sharhin Xi Kan Ciyar Da Zamanantar Da Kasar Sin Gaba

Related

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu
Nishadi

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

7 days ago
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 
Nishadi

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

2 weeks ago
Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani
Nishadi

Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani

3 weeks ago
Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa
Nishadi

Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa

3 weeks ago
Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro
Nishadi

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

4 weeks ago
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage
Nishadi

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

4 weeks ago
Next Post
Za A Wallafa Sharhin Xi Kan Ciyar Da Zamanantar Da Kasar Sin Gaba

Za A Wallafa Sharhin Xi Kan Ciyar Da Zamanantar Da Kasar Sin Gaba

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.