• English
  • Business News
Friday, May 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Kasuwa 40 Sun Rasu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Kebbi

by Abubakar Abba
2 years ago
in Manyan Labarai
0
‘Yan Kasuwa 40 Sun Rasu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kimanin ‘yan kasuwa 40 ne suka rasu a hatsarin jirgin ruwa a kogin Neja a yayain da suke akan hanyarsu ta zuwa karamar hukumar Yauri da ke a jihar Kebbi. 

An ruwaito cewa, jirgin wanda ke dauke da ‘yan kasuwa su 50 tare da hajarsu ya taso ne daga kauyen Kasabo zuwa garin Yauri a ranar Litinin don zuwa cin kasuwa, inda bayan Igiyar ruwa ta kada, ya kife.

  • MDD Da NSCC Sun Yi Bikin Ranar Tsofaffi Ta Duniya Ta 2023
  • Juyin Mulki: An Sake Bude Makarantu A Nijar Bayan Wata 3

Sai dai, an ruwaito cewa, masu ceto, sun samu nasarar ceto mutum 10 inda kuma har yanzu, ba a iya gano fasinjiji 40 ba.

Bugu da kari, an ruwato cewa, a ranar Talata an samu nasarar gano gawarwakin fasinjoji shida.

Rahotanni sun sanar da cewa, a watan Satumbar da ya wuce, kimanin mutane guda 936 suka rasu a hatsarin jirgin ruwa daban-,daban a sassan kasar nan.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano

Shugaban karamar hukumar Yauri, Alhaji Bala Mohammed wanda ya tabbatar da adadin fasinjojin da suka rasu, ya sanar da cewa, har yanzu masu ceto na kan ci gaba da neman sauran fasinjojin da suka bace a cikin kogin.

Kazalika a ta’aziyyarsa a lokacin da ya kai ziyara a garin na Yauri a ranar Litinin, gwamnan jihar Nasiru Idris, ya yi addu’ar fatan samun lafiya ga fasinjojin da suka samu raunuka tare da yin fatan kare sake aukuwar hatsarin a nan gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FasinjojiHatsarin Jirgin RuwaKebbi
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Sake Kashe Mutane 3 A Wani Sabon Hari A Sakkwato

Next Post

Ranar ‘Yanci: ‘Yan Nijeriya Mazauna Landan Sun Nemi A Yi Wa Gwamnatin NNPP Adalci A Kano

Related

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

2 hours ago
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano
Manyan Labarai

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano

4 hours ago
Duk Da Janye Tallafin Rarar Mai, Matsin Rayuwa Na Addabar ‘Yan Nijeriya
Manyan Labarai

Duk Da Janye Tallafin Rarar Mai, Matsin Rayuwa Na Addabar ‘Yan Nijeriya

8 hours ago
Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa
Manyan Labarai

Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa

9 hours ago
Yadda Rikici Ya Yi Sanadin Kashe DPO A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano

21 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa

24 hours ago
Next Post
NNPP

Ranar 'Yanci: 'Yan Nijeriya Mazauna Landan Sun Nemi A Yi Wa Gwamnatin NNPP Adalci A Kano

LABARAI MASU NASABA

Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

May 30, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Tattaunawa Ta Hudu Kan Musaya Da Koyi Da Juna A Tsakanin Al’ummomi Ta Fannin Wayewar Kansu

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Tattaunawa Ta Hudu Kan Musaya Da Koyi Da Juna A Tsakanin Al’ummomi Ta Fannin Wayewar Kansu

May 30, 2025
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

May 30, 2025
Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 60 A Borno

May 30, 2025
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano

May 30, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 30-03-2025

May 30, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ƴan Daba 33 A Kano

An Kama Mutane 49 Da Ake Zargi Da Damfara A Jihar Kogi

May 30, 2025
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (2)

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (2)

May 30, 2025
Duk Da Janye Tallafin Rarar Mai, Matsin Rayuwa Na Addabar ‘Yan Nijeriya

Duk Da Janye Tallafin Rarar Mai, Matsin Rayuwa Na Addabar ‘Yan Nijeriya

May 30, 2025
Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa

Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa

May 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.