• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Jinjina Wa Kamfanin BUA Bisa Karya Farashin Buhun Siminti Zuwa Naira 3,500

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
BUA

Gwamnatin tarayya ta jinjina wa kamfanin siminti na BUA bisa karya farashin buhun siminti daga naira 5,500 zuwa 3,500.

Da yake yaba wa kamfanin, ministan gidaje da raya birane, Ahmed Musa Dangiwa, ya bayyana cewa wannan shiri da aka yi zai rage tsadar siminti, wanda ke da tsada wajen gina gidaje.

  • Huldar Banki Da Babu Ruwa: Bankin TAJ Ya Samu Ribar Naira Biliyan 6 A Zangon Farko
  • Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Wa Matar Da ‘Yan Bindiga Suka Raba Da Muhallinta Shatara Ta Arziki

A cewarsa, zai goyi bayan ajandar Shugaba Kasa Bola Tinubu na samar da gidaje masu sauki ga ‘yan Nijeriya.

Ministan ya bayyana haka ne a matsayin martani ga sanarwar da kamfanin BUA ya bayar a ranar 1 ga Oktoba, 2023 a hukumance ta rage farashin siminti a Nijeriya.

Ya kara da cewa tsadar siminti ya haifar da tashin gwauron zabi na gidaje, wanda hakan ya sa talakawan Nijeriya ba za su iya biya ba. Ministan ya kara da cewa matakin na kamfanin BUA wani gagarumin ci gaba na saukaka kudi a kan masu neman gida.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

Dangiwa ya jaddada cewa tun da ya hau kujerar  minista, ya fara inganta samar da gidaje masu saukin kudi a matsayin babban abin da ya bai wa fifiko bisa tsarin ajandar shugaban kasa.

“Tashin farashin kayayyakin gine-gine, musamman siminti, ya kawo cikas ga ‘yan Nijeriya masu bukatar mallakar gidaje. Matakin da kamfanin BUA ya dauka na rage farashin siminti zuwa naira 3,500 abin yabawa ne matuka. Ya nuna fahimtar gwagwarmayar da talakawan Nijeriya ke fuskanta kuma mataki ne mai kyau na samar da gidaje mafi araha da kowa ke bukata.

“Na yaba wa kamfanin BUA saboda shawarar da ya yanke na rage farashin siminti. Matsuguni masu araha hakki ne na asali kuma wannan matakin ba shakka zai rage kalubalen da ‘yan kasar ke fuskanta. Yana nuna sadaukarwar da aka yi na inganta rayuwar al’ummarmu da kuma cimma muradin bukasa burane,” in ji shi.

Dangiwa ya bukaci sauran kamfanoni su yi koyi da BUA, inda ya bukace su da su yi la’akari da tasirin yadda wannan mataki zai bukasa rayuwar al’umma.

Ya bayyana kokarin hadin gwiwa tsakanin gwamnati da kamfanoni masu zaman kansu wajen magance matsaloli rashin mallakar muhalli ga dukkan ‘yan Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 
Labarai

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025
gaza
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

October 28, 2025
Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani
Ra'ayi Riga

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

October 28, 2025
Next Post
Manyan Ayyukan Da Ke Gaban Sabon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya

Kwarewar Sabon Shugaban Babban Bankin Nijeriya (CBN)

LABARAI MASU NASABA

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025
Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

October 28, 2025
Xi Ya Yi Karin Haske Kan Muhimman Shawarwarin Da Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Yayin Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15

Xi Ya Yi Karin Haske Kan Muhimman Shawarwarin Da Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Yayin Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15

October 28, 2025
gaza

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

October 28, 2025
Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

October 28, 2025
Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

October 28, 2025
Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.