ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Wa Matar Da ‘Yan Bindiga Suka Raba Da Muhallinta Shatara Ta Arziki

by Leadership Hausa
3 years ago
gwamna

LABARAI MASU NASABA

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

A jiya Alhamis ne Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara ya karɓi baƙuncin matar nan da ‘yan bindiga suka raba da muhallinta da aka yaɗa a wani faifan bidiyo.
Faiaifan bidiyon ya nuna wata uwa da ‘ya’yanta tana bayani a kan ‘yan bindiga suka tilasta musu cin ciyawa domin su tsira da rayukansu.
Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar ta Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta ce halin da matar wacce ta rasa matsugunin ke ciki ya nuna cewa akwai bukatar a ɗauki matakin gaggawa don magance musabbabin Ibtila’in da yake raba mutane da muhallansu same su da kuma samar matakawuna da kuma tabbatar da cewa iyalai suna samun abubuwan bukata na rayuwa.

  • Tirka-tirkan Takardun Tinubu: Ku Zo Mu Hada Hannu Don Fafutukar Wanzar Da Gaskiya – Atiku Ya Roki Obi, Kwankwaso
  • NIS Ta Samar Da Fasfo 204,332 Cikin Mako Uku – Adepoju

Ta ƙara da cewa Gwamnan ya karɓi baƙuncin matar da ta rasa muhallin nata ne a matsayin nuni kan jajircewarsa wajen kare rayuka da dukiyoyin al’ummar Zamfara.

gwamna
“A yau (Alhamis) ne Gwamna Dauda Lawal ya karbi baƙuncin Hauwa’u Halliru, wadda ta rasa komi a dalilin tu’annatin ‘yan fashin daji.
“Gwamna Lawal ya bayyana ƙudirinsa na kawo ƙarshen rashin tsaro a jihar tare da jajanta wa iyalan da ɓarnar ‘yan fashin dajin ta shafa.
“A matsayinsa na shugaba mai tausayi, Gwamna Lawal ya gaggauta samar wa matar da ta rasa muhallin nata gida mai kyau da aka sa wa komai na more rayuwa.
“Ya kuma tabbatar mata da kudirin gwamnatinsa na ciyar da iyalinta abinci da sauran abubuwan bukatu, ta yadda za ta sake gina rayuwarta cikin mutunci da tsaro.
“Bugu da kari, gwamnan ya umarci kwamishinan ilimi, kimiya da fasaha da ya tabbatar da shigar da ‘ya’yanta makaranta cikin gaggawa da kuma samun cikakken tallafin karatu.

ADVERTISEMENT

“Ya kuma bukaci dukkan hukumomin da abin ya shafa da su ƙara ƙaimi wajen zakulo iyalai marasa galihu da ke fuskantar irin wannan ƙalubale tare da ba su tallafin da ya dace.
“A nasa jawabin, Shugaban Ƙungiyar Masu Kare Hakkin Bil’adama, Kwamared Salisu Umar, ya bayyana matukar jin daɗinsa kan yadda Gwamnan Jihar Zamfara ke ƙoƙarin tabbatar da tsaro da jin daɗin jama’a.
“Ya kuma yaba da yadda gwamnan ya nuna himma, tare da bayyana cewa wannan ne karon farko da ya ga irin wannan kyakkyawar shugabanci a jihar, inda ya ƙara da cewa kalaman nasa sun yi daidai da ra’ayoyin jama’a, wadanda suka dade suna jiran shugaban da zai riƙa sanya buƙatunsu a gaba.” In ji sanarwar.

gwamna
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi
Manyan Labarai

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

July 6, 2026
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

July 6, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

July 6, 2026
Next Post
Shawarar Kasar Sin Ta Gina Al’ummar Duniya Mai Mokamar Bai Daya

Shawarar Kasar Sin Ta Gina Al’ummar Duniya Mai Mokamar Bai Daya

LABARAI MASU NASABA

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

July 6, 2026
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

July 6, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

July 6, 2026
Gwamnatin Kano Ta Kashe Biliyan 928 A Ayyukan Ci Gaba 1,508

Gwamnatin Kano Ta Kashe Biliyan 928 A Ayyukan Ci Gaba 1,508

July 6, 2026
Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

July 6, 2026
FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.