ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Wa Matar Da ‘Yan Bindiga Suka Raba Da Muhallinta Shatara Ta Arziki

by Leadership Hausa
3 years ago
gwamna

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

A jiya Alhamis ne Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara ya karɓi baƙuncin matar nan da ‘yan bindiga suka raba da muhallinta da aka yaɗa a wani faifan bidiyo.
Faiaifan bidiyon ya nuna wata uwa da ‘ya’yanta tana bayani a kan ‘yan bindiga suka tilasta musu cin ciyawa domin su tsira da rayukansu.
Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar ta Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta ce halin da matar wacce ta rasa matsugunin ke ciki ya nuna cewa akwai bukatar a ɗauki matakin gaggawa don magance musabbabin Ibtila’in da yake raba mutane da muhallansu same su da kuma samar matakawuna da kuma tabbatar da cewa iyalai suna samun abubuwan bukata na rayuwa.

  • Tirka-tirkan Takardun Tinubu: Ku Zo Mu Hada Hannu Don Fafutukar Wanzar Da Gaskiya – Atiku Ya Roki Obi, Kwankwaso
  • NIS Ta Samar Da Fasfo 204,332 Cikin Mako Uku – Adepoju

Ta ƙara da cewa Gwamnan ya karɓi baƙuncin matar da ta rasa muhallin nata ne a matsayin nuni kan jajircewarsa wajen kare rayuka da dukiyoyin al’ummar Zamfara.

gwamna
“A yau (Alhamis) ne Gwamna Dauda Lawal ya karbi baƙuncin Hauwa’u Halliru, wadda ta rasa komi a dalilin tu’annatin ‘yan fashin daji.
“Gwamna Lawal ya bayyana ƙudirinsa na kawo ƙarshen rashin tsaro a jihar tare da jajanta wa iyalan da ɓarnar ‘yan fashin dajin ta shafa.
“A matsayinsa na shugaba mai tausayi, Gwamna Lawal ya gaggauta samar wa matar da ta rasa muhallin nata gida mai kyau da aka sa wa komai na more rayuwa.
“Ya kuma tabbatar mata da kudirin gwamnatinsa na ciyar da iyalinta abinci da sauran abubuwan bukatu, ta yadda za ta sake gina rayuwarta cikin mutunci da tsaro.
“Bugu da kari, gwamnan ya umarci kwamishinan ilimi, kimiya da fasaha da ya tabbatar da shigar da ‘ya’yanta makaranta cikin gaggawa da kuma samun cikakken tallafin karatu.

ADVERTISEMENT

“Ya kuma bukaci dukkan hukumomin da abin ya shafa da su ƙara ƙaimi wajen zakulo iyalai marasa galihu da ke fuskantar irin wannan ƙalubale tare da ba su tallafin da ya dace.
“A nasa jawabin, Shugaban Ƙungiyar Masu Kare Hakkin Bil’adama, Kwamared Salisu Umar, ya bayyana matukar jin daɗinsa kan yadda Gwamnan Jihar Zamfara ke ƙoƙarin tabbatar da tsaro da jin daɗin jama’a.
“Ya kuma yaba da yadda gwamnan ya nuna himma, tare da bayyana cewa wannan ne karon farko da ya ga irin wannan kyakkyawar shugabanci a jihar, inda ya ƙara da cewa kalaman nasa sun yi daidai da ra’ayoyin jama’a, wadanda suka dade suna jiran shugaban da zai riƙa sanya buƙatunsu a gaba.” In ji sanarwar.

gwamna
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
  • Leadership Hausa
    Batun Dawo Da Tallafin Mai Da Atiku Ya Yi Na Ci Gaba Da Tayar Da Kura
  • Leadership Hausa
    Batun Guguwar Kakar Yakin Neman Zabukan 2027 A Nijeriya

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Shawarar Kasar Sin Ta Gina Al’ummar Duniya Mai Mokamar Bai Daya

Shawarar Kasar Sin Ta Gina Al’ummar Duniya Mai Mokamar Bai Daya

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.