• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wata Shawarar Dake Amfanar Daukacin Duniya

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Wata Shawarar Dake Amfanar Daukacin Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Najeriya kasa ce da ta fi karfin tattalin arziki a nahiyar Afirka, kana muhimmiyar cibiyar ciniki ce a yammacin Afirka. Sai dai duk da haka, kasar ta dade tana fama da matsalar karancin wata babbar tashar jiragen ruwa, inda ake samun ruwan teku mai zurfi. Daga baya, a farkon wannan shekarar da muke ciki, an fara amfani da tashar jiragen ruwa ta Lekki, wadda wani kamfanin kasar Sin ya gina, wanda hakan ya kawo karshen wannan mawuyacin halin da Najeriya ke ciki. Ana kuma sa ran ganin wannan sabuwar tasha ta samar da kudin shiga da zai kai dalar Amurka biliyan 360, da guraben aikin yi dubu 170, ga Najeriya. To, idan mun duba sauran kasashen Afirka, gami da na duniya baki daya, za mu iya ganin dimbin misalan da suka yi kama da tashar jiragen ruwa ta Lekki, inda hadin gwiwar da aka yi tare da kasar Sin ke haifar da damammakin samun ci gaban tattalin arziki.

Ko me ya sa hadin gwiwa da Sin ya ke samar da hakikanin ci gaba? Dalili shi ne, kasar Sin tana da wani tsari mai muhimmanci na hadin gwiwa da sauran kasashe, da ake kira shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya”. A yau ne kuma, ofishin aikin watsa labarai na majalisar gudanarwar kasar Sin ya fitar da wata takardar bayani, wadda ta bayyana sakamakon da shawarar ta haifar cikin shekaru 10 da suka gabata, da gudunmowarta ta fuskar kare zaman lafiya da tabbatar da ci gaban duniya.

  • Layin Dogo Tsakanin Sin Da Turai Ya Zama Babban Aiki Da Ma Alamar Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”
  • Dan Kwallon Nijeriya Na Cikin Hazikan ‘Yan Wasan Bundesliga Na Watan Satumba

A shekarar 2013, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da ra’ayi na “Gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya”, inda ya jaddada muhimmancin hadin kan mabambantan al’ummu, da ba su damar cimma moriya da ci gaba tare. Ban da haka, shugaban ya yi amfani da sunayen wasu hanyoyin ciniki da cudanyar al’adu guda 2 masu muhimmanci a tarihi, wajen kirkiro sunan shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya”, wadda ya gabatar da ita a matsayin dandalin aiwatar da ra’ayin “Kafa al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya”. Sa’an nan ruhin shawarar ya hada da: Tattaunawa bisa daidaito don tabbatar da ganin kowa ya ci moriya, da bude kofa ga duk wanda ke son halarta, maimakon kulla karamin kawance da nufin yi wa wasu saniyar ware. Sauran manufofin da shawarar ta kunsa sun hada da magance cin hanci da rashawa, da kare muhalli, da samun ci gaba mai dorewa, da haifar wa jama’ar kasashe daban daban da hakikanin alfanu, da dai sauransu.

Ko wadannan ra’ayoyi da manufofi suna da amfani? Sai an aiwatar da su, daga baya za a gani. Yadda ake aiwatar da shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya” ya shafi bangarorin hada kayayyakin more rayuwa, da tsare-tsaren gudanar da ayyuka na mabambantan kasashe, gami da tabbatar da zumunta da kauna tsakanin jama’arsu. Bisa wannan shawara, kasar Sin ta kulla yarjeniyoyin hadin gwiwa fiye da 200 tare da kasashe fiye da 150 da kungiyoyin kasa da kasa fiye da 30, cikin shekaru 10 da suka wuce. Kana a nahiyar Afirka kadai, shawarar ta kai ga gina wata babbar cibiyar kandagarkin cututtuka ta Afirka ta zamani a Addis Ababa, fadar mulkin kasar Habasha, inda hedkwatar kungiyar kasashen Afirka ta AU take; da kuma baiwa manoman kasashen Afirka damar fitar da karin kayayyakinsu zuwa kasar Sin don samun karin kudin shiga.

Ban da haka, shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya” ta sa kasar Congo Brazaville samun wani babban bankin kasuwanci na kanta, da sanya kasar Zambia samun jarin da yawansa ya zarce dalar Amurka biliyan 2.5, da guraben aikin yi fiye da dubu 10, bisa yankin raya tattalin arziki da ciniki da kasar Sin ta gina a kasar, gami da baiwa mutanen kauyuka 9512 na kasashe 21 dake nahiyar Afirka damar kallon telabijin a gidajensu…

Labarai Masu Nasaba

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Haka zalika, za mu iya fahimtar salon kasar Sin a fannin gudanar da ayyuka, ta hanyar nazari kan takardar bayani da aka gabatar a wannan karo. Wato, da farko shugabannin kasar za su gabatar da wani nagartaccen ra’ayi ko kuma tsarin aiki, daga bisani dukkan al’ummun kasar za su dade suna kokarin aiwatar da tsarin aikin a kai a kai, inda ba za a gabatar da wani tsarin aiki ba tare da aiwatar da shi ba, kana ba za a manta da burin da aka sanya, da ra’ayin da aka gabatar tun da farko ba. Saboda haka, ana ganin yadda shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya” ta kasar Sin, da ra’ayinta na “Gina al’ummar dan Adam mai makomar bai daya” ke haifar da ci gaba a kasashe daban daban, kana tabbas za a ci gaba da ganin abkuwar haka a nan gaba. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CGTNCMGCRI Hausa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Layin Dogo Tsakanin Sin Da Turai Ya Zama Babban Aiki Da Ma Alamar Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

Next Post

Kotun Soji Ta Yanke Wa Manjo Janar Mohammed Hukuncin Daurin Shekaru 7 A Gidan Yari

Related

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

21 minutes ago
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

2 hours ago
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa
Daga Birnin Sin

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

3 hours ago
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata
Daga Birnin Sin

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

4 hours ago
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

22 hours ago
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

23 hours ago
Next Post
Kotun Soji Ta Yanke Wa Manjo Janar Mohammed Hukuncin Daurin Shekaru 7 A Gidan Yari

Kotun Soji Ta Yanke Wa Manjo Janar Mohammed Hukuncin Daurin Shekaru 7 A Gidan Yari

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.