ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

- Ya Ce Zamfara Tana Kan Sabuwar Turba

by Sulaiman
9 months ago
Gwamna lawal

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya tabbatar wa ’yan kasuwa na cikin gida cewa jihar na kan wata sabuwar turba kuma tana samun ci gaba sosai, inda ta ke sauyawa daga jihar da ƙalubale suka mamaye ta.

 

Gwamnan ya ƙaddamar da rabon tallafin a ƙarƙashin shirin SABER (SERBS) a ranar Alhamis a sakatariyar JB Yakubu da ke Gusau.

ADVERTISEMENT
  • ‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja
  • Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa shirin gwamnatin jihar kan kawo sauyi kan harkokin kasuwanci (SABER) na nuna da wani gagarumin ci gaba a habaka tattalin arzikin jihar.

 

LABARAI MASU NASABA

Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

Sanarwar ta ƙara da cewa, SABER wani shiri ne na shekaru biyar, wanda ya dogara da aiki, wanda Bankin Funiya ke tallafawa, wanda aka tsara shi cikin tsanaki domin wargaza shingayen faɗuwar jari, da zaburar da sana’o’i masu zaman kansu, da samar da ayyukan yi masu ɗorewa ga al’ummar Zamfara.

 

Za a raba Naira 150,000 ga mutum 2,000 a faɗin jihar domin tallafa wa ƙananan sana’o’i. Bugu da ƙari, mutane 1,000 a ƙanana da matsakaitan sana’o’i za su karbi Naira 500,000 kowanne. Haka kuma, mutane 60 daga matsakaita da manyan ‘yan kasuwa za su ci gajiyar tallafin Naira miliyan biyar kowannen su.

Gwamna lawal

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya bayyana cewa, SABER ba wani abu ba ne na yau da kullum, inda ya tabbatar da cewa adadin kuɗaɗen da aka ware domin gudanar da ayyukan shirin ya kai kusan Naira Biliyan 1.1, tare da tallafin da ya kai dalar Amurka miliyan 20 zuwa dala miliyan 52 tsakanin shekarar 2022 zuwa 2026.

 

“Mun taru ne a yau domin ƙaddamar da shirin tare da fara bayar da kuɗaɗe don tallafa wa ‘yan kasuwa da mata daban-daban a fafin jihar nan.

 

“Akwai manyan nau’o’i uku na kuɗaɗen da za a biya, mun yi nazari sosai kan cibiyoyin gwamnati da kuma kamfanoni masu zaman kansu, waɗanda shugabannin ƙungiyar ‘yan kasuwa ke wakilta, don zabar waɗanda za su ci gajiyar kowane fanni na tallafin.

 

Gwamna Lawal ya ci gaba da jaddada cewa shirin na SABER wanda ma’aikatar kasafin kuɗi da tsare-tsare ta shirya shi, ma’aikatu daban-daban ne ke aiwatar da shi, waɗanda suka haɗa da ma’aikatar kasuwanci da masana’antu, ZAGIS, da sauran su kamar kuɗi, noma, da shari’a. Hakanan ya ƙunshi ayyuka na Harajin Cikin Gida, Kamfanin Gidaje, da ZITDA, suna aiki tare don samar da sauƙin kasuwanci.

 

Tun da farko, Babban Darakta na Hukumar Raya Ƙanana da Matsakaitan Masana’antu ta Nijeriya (SMEDAN), Charles Odii, ya yaba wa Gwamna Dauda Lawal bisa ɗimbin ƙoƙarinsa na tallafa wa ‘yan kasuwa na cikin gida a Jihar Zamfara.

 

“Na ji daɗin yadda gwamna ke bakin ƙoƙarinsa wajen bunƙasa ƙananan sana’o’i a Nijeriya, ina zaune na ji cewa ‘yan kasuwa 2,000 za su samu Naira 150,000. Ina ganin yana da muhimmanci idan ƙaramin ɗan kasuwa ya samu Naira 150,000, zai ɗauki mutum ɗaya aiki.

Gwamna lawal
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
  • Sulaiman
    Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
  • Sulaiman
    Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines
  • Sulaiman
    Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

MASU ALAKA

Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare
Labarai

Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare

June 12, 2026
Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

June 12, 2026
Samar Da Abinci:Jihar Nasarawa Ta Fara Shirin Gina Kananan Madatsun Ruwa
Labarai

Samar Da Abinci:Jihar Nasarawa Ta Fara Shirin Gina Kananan Madatsun Ruwa

June 12, 2026
Next Post
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

LABARAI MASU NASABA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026
Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare

Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare

June 12, 2026
Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

June 12, 2026
Samar Da Abinci:Jihar Nasarawa Ta Fara Shirin Gina Kananan Madatsun Ruwa

Samar Da Abinci:Jihar Nasarawa Ta Fara Shirin Gina Kananan Madatsun Ruwa

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.