• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Damu Matuka Kan Ta’azzarar Rikici Da Tasirinsa Kan Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gabas Ta Tsakiya

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Ta Damu Matuka Kan Ta’azzarar Rikici Da Tasirinsa Kan Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gabas Ta Tsakiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin, ya bayyana a yayin taron manema labaru na yau da kullum Alhamis din nan cewa, kasar Sin tana bakin ciki matuka da yadda rikicin da ke faruwa a halin yanzu tsakanin Palasdinu da Isra’ila, ya haifar da hasarar rayukan fararen hula da ba su ji ba ba su gani ba, tare da nuna matukar damuwa game da tabarbarewar yanayin tsaro da ma jin kai a yankin Falasdinu, ta kuma damu matuka game da mummunan tasirin da tashin hankalin zai haifar ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

Wang Wenbin ya bayyana cewa, kasar Sin ta lura cewa, kungiyar hadin kan kasashen Larabawa ta gudanar da taron gaggawa na ministocin harkokin wajen kungiyar, inda ta zartas da wani kuduri dake goyon bayan kungiyar wajen taka muhimmiyar rawa kan batun Palasdinu.

  • Shugaba Xi Ya Yi Rangadi A Biranen Jingdezhen Da Shangrao Na Lardin Jiangxi 
  • Kungiyar Kasashen Larabawa Ta Yi Taro Kan Rikicin Isra’ila da Falasdinu

Kasar Sin da kasashen Larabawa na da kusan ra’ayi daya kan batun Falasdinu, inda bangarorin biyu suka yi kira da a hanzarta tsagaita bude wuta da kawo karshen hare-haren bama-bamai, da yin Allah wadai da ayyukan dake cutar da fararen hula, da kaucewa ta’azzarar al’amura da haddasa bala’in jin kai.

Wang Wenbin ya ce, kasar Sin tana son ci gaba da yin mu’amala da hadin gwiwa tare da dukkan bangarorin kungiyar hadin kan kasashen Larabawa, da sa kaimi ga yin shawarwarin zaman lafiya, da kokarin maido da shirin zaman lafiya a yankin Gabas ta Tsakiya kan turba mai kyau.

Bugu da kari, a jiya manzon musamman na kasar Sin kan batun Gabas ta tsakiya Mr. Zhai Jun ya tattauna kan yanayin da Palestinu da Isra’ila ke ciki tare da mataimakiyar ministan harkokin wajen kasar Palestinu ta farko Amal Jadou ta wayar tarho, inda Zhai Jun ya bayyana cewa, kasar Sin ta damu matuka da rasuwar fararen hula da dama sakamakon rikicin Palestinu da Isra’ila.

Labarai Masu Nasaba

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Ya kara da cewa, yanzu abu mafi muhimmanci shi ne, a tsaigaita bude wuta nan take. Kuma kamata ya yi kasashen duniya su yi kokari domin sassauta rikicin, tare kuma da samar da taimakon jin kai ga al’ummar Palestinu. Ya ce kasar Sin za ta ci gaba da yin kokari domin cimma burin tsagaita bude wuta tsakanin sassan biyu, tare kuma da samar da tallafi domin sassauta rikicin jin kai, kana za ta ci gaba da shawo kan sassan biyu, su komawa shawarwarin wanzar da zaman lafiya, ta yadda za a daidaita batun Palestinu bisa adalci daga duk fannoni.

A na ta bangare, Jadou ta gode wa kasar Sin bisa matsayin adalcin da take kai game da batun Palestinu. A cewarta, Palestinu ta na da cikakken imani da kasar Sin, kuma tana fatan kasar Sin za ta ci gaba da taka rawar gani kan batun a halin da ake ciki yanzu. (Mai fassara: Ibrahim Yaya, Jamila Zhou)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FalasdinuGabas ta TsakiyaIsra'ila
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugabannin Kasashen Duniya Na Cike Da Kyakkyawan Fata Game Da Taron Raya Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya

Next Post

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ta Kasance Mai Asali Daga Sin Amma Mai Rungumar Dukkanin Duniya

Related

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

60 minutes ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

2 hours ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

3 hours ago
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka
Daga Birnin Sin

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

4 hours ago
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154
Daga Birnin Sin

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

5 hours ago
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan
Daga Birnin Sin

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

6 hours ago
Next Post
Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ta Kasance Mai Asali Daga Sin Amma Mai Rungumar Dukkanin Duniya

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ta Kasance Mai Asali Daga Sin Amma Mai Rungumar Dukkanin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.